Aminiya:
2025-09-17@23:15:07 GMT

Ambaliyar ruwa ta tsayar da ababen hawa cak a tsakiyar birnin Abuja

Published: 12th, September 2025 GMT

An samu ambaliyar ruwa a tituna da dama na tsakiyar Babban Birnin Tarayya Abuja sakamakon mamakon ruwan saman da aka tafka da safiyar Alhamis.

Yankunan da ambaliya ta fi shafa sun hada da Asokoro, Guzape, Jabi, Kado da kuma Wuse.

Wasu direbobi da suka zanta da Aminiya sun ce sun sha wahala wajen samun hanyar wucewa a unguwannin Asokoro da Guzape yayin ruwan saman.

Jonathan ya tattauna da Peter Obi kan tsayawa takara a 2027 Likitoci sun yi barazanar sake tsunduma yajin aiki

A wani bidiyo da wani mai suna Prince Adebisi Adetunji ya wallafa a shafinsa na Facebook, an ga yadda ruwan ya mamaye titin Asokoro, inda direbobi da mazauna yankin suka yi ta kokarin yadda za su tsallake ruwan.

Ambaliyar dai ta kawo cikas ga zirga-zirgar ababen hawa, inda aka ga motoci na ta kokarin ketare ruwan da ya mamaye titunan.

Mazauna yankin sun ce rashin ingantaccen tsarin magudanun ruwa ne ya kara dagula lamarin.

Wani direba mai suna  Musa Ibrahim, ya shaida wa wakilinmu cewa tituna da dama a Asokoro da Guzape sun ki biyuwa, lamarin da ya haddasa cunkoso.

Shi ma wani direban, Emmanuel Peter, ya ce shi da wasu direbobin sai da suka jira na wani lokaci kafin daga bisani su samu wata hanyar da ba ta da hatsari su bi.

“Ya kamata hukumar birnin ta nemo mafita kan matsalar magudanun ruwa a birnin tarayya,” in ji Peter.

A cewarsa, matsalar ba ta tsaya ga Asokoro da Guzape kadai ba, domin tana faruwa a kusan dukkan unguwanni idan aka yi ruwan sama mai yawa.

“Hakan na faruwa a Jabi, Wuse, har ma da yankin Central Area a duk shekara. Dole ne masu kula da birnin su dauki mataki kan wannan matsala,” in ji shi.

Wani bangare na titin Obafemi Awolowo da ke Jabi ma ya cika da ruwa yayin ambaliyar.

An ga direbobi da dama suna kokarin ketare ruwan da ya mamaye titin.

Alhaji Nuhu Ademola ya ce motarsa ta makale a cikin ruwan a kusa da tashar motar Jabi.

A cewarsa, ya dauki kusan minti 30 kafin ruwan ya ragu sannan ya samu damar fita da motarsa.

Alhaji Ademola ya bukaci hukumar birnin da ta nemo mafita mai dorewa kan matsalar ambaliyar ruwa a birnin na Abuja.

“Ai ba sai mun fada musu ba, su ma suna gani. Yaya za a gina birnin tarayya ba tare da tsarin magudanar ruwa mai kyau da tsari ba?” in ji shi.

Wakilinmu ya rawaito cewa an kuma samu irin wannan ambaliya a yankin Life Camp da kuma Wuse.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa