Ambaliyar ruwa ta tsayar da ababen hawa cak a tsakiyar birnin Abuja
Published: 12th, September 2025 GMT
An samu ambaliyar ruwa a tituna da dama na tsakiyar Babban Birnin Tarayya Abuja sakamakon mamakon ruwan saman da aka tafka da safiyar Alhamis.
Yankunan da ambaliya ta fi shafa sun hada da Asokoro, Guzape, Jabi, Kado da kuma Wuse.
Wasu direbobi da suka zanta da Aminiya sun ce sun sha wahala wajen samun hanyar wucewa a unguwannin Asokoro da Guzape yayin ruwan saman.
A wani bidiyo da wani mai suna Prince Adebisi Adetunji ya wallafa a shafinsa na Facebook, an ga yadda ruwan ya mamaye titin Asokoro, inda direbobi da mazauna yankin suka yi ta kokarin yadda za su tsallake ruwan.
Ambaliyar dai ta kawo cikas ga zirga-zirgar ababen hawa, inda aka ga motoci na ta kokarin ketare ruwan da ya mamaye titunan.
Mazauna yankin sun ce rashin ingantaccen tsarin magudanun ruwa ne ya kara dagula lamarin.
Wani direba mai suna Musa Ibrahim, ya shaida wa wakilinmu cewa tituna da dama a Asokoro da Guzape sun ki biyuwa, lamarin da ya haddasa cunkoso.
Shi ma wani direban, Emmanuel Peter, ya ce shi da wasu direbobin sai da suka jira na wani lokaci kafin daga bisani su samu wata hanyar da ba ta da hatsari su bi.
“Ya kamata hukumar birnin ta nemo mafita kan matsalar magudanun ruwa a birnin tarayya,” in ji Peter.
A cewarsa, matsalar ba ta tsaya ga Asokoro da Guzape kadai ba, domin tana faruwa a kusan dukkan unguwanni idan aka yi ruwan sama mai yawa.
“Hakan na faruwa a Jabi, Wuse, har ma da yankin Central Area a duk shekara. Dole ne masu kula da birnin su dauki mataki kan wannan matsala,” in ji shi.
Wani bangare na titin Obafemi Awolowo da ke Jabi ma ya cika da ruwa yayin ambaliyar.
An ga direbobi da dama suna kokarin ketare ruwan da ya mamaye titin.
Alhaji Nuhu Ademola ya ce motarsa ta makale a cikin ruwan a kusa da tashar motar Jabi.
A cewarsa, ya dauki kusan minti 30 kafin ruwan ya ragu sannan ya samu damar fita da motarsa.
Alhaji Ademola ya bukaci hukumar birnin da ta nemo mafita mai dorewa kan matsalar ambaliyar ruwa a birnin na Abuja.
“Ai ba sai mun fada musu ba, su ma suna gani. Yaya za a gina birnin tarayya ba tare da tsarin magudanar ruwa mai kyau da tsari ba?” in ji shi.
Wakilinmu ya rawaito cewa an kuma samu irin wannan ambaliya a yankin Life Camp da kuma Wuse.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliya
এছাড়াও পড়ুন:
An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
’Yan sanda a jihar Legas sun kama wani tsohon fursuna tare da wasu mutum biyu bisa zargin hannu a jerin laifukan fashi da yankan aljihu a jihar kwana biyar da fitowa daga kurkuku.
Tsohon fursunan mai shekaru 25 da haihuwa, Segun Kolawole, an kama shi ne bayan kwana biyar da aka sako shi daga cibiyar gyaran hali ta Kirikiri, a jihar Legas.
Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano SpalletiSauran wadanda aka kama tare da shi sun haɗa da Sodiq Isa mai shekaru 27 da Adekanmbi Ganiu mai shekaru 21.
Rahotanni sun nuna cewa an kama waɗanda ake zargin ne bisa laifukan yankan aljihun mutane da sauran laifukan sata a sassa daban-daban na jihar.
Mai magana da yawun ’yan sandan jihar, SP Abimbola Adebisi, ta tabbatar da cafke Kolawole, inda ta ce an kama shi da misalin ƙarfe 8 na safiyar Talata a kasuwar Oshodi, bayan jami’ai sun lura da motsinsa da ya zama abin zargi.
Adebisi ta ce an same shi da tsabar kuɗi ₦80,000 da wayar Infinix Note 40 Pro, waɗanda aka gano daga wani fashi da ya aikata a Opebi, inda ake zargin ya saci ₦200,000 da wayar daga hannun wani ɗan kasuwa da ke barci.
“Bincike ya ƙara tabbatar da cewa ya riga ya sayi sabbin kaya da takalma da wani ɓangare na kuɗin da ya sata, waɗanda suma aka kwato su daga hannunsa,” in ji ta.
Haka kuma, a wani samame daban da aka gudanar da misalin ƙarfe 5 na yamma a ranar Juma’a, jami’an RRS sun kama Sodiq Isa da Adekanmbi Ganiu bisa zargin yunkurin satar wayoyin hannu daga hannun fasinjoji a sassa daban-daban na Legas.