An saki fursunonin siyasa 52 a Belarus
Published: 11th, September 2025 GMT
Gwamnatin Belarus ƙarƙashin jagorancin Shugaba Alexander Lukashenko ta saki fursunoni siyasa 52 ciki har da fitaccen ɗan adawa, Mikola Statkevich da kuma ɗan jarida Ihar Losik, a wani yunƙuri da aka danganta da ruwa da tsakin Amurka.
Shugaban Lithuania, Gitanas Nauseda, ne ya bayyana hakan a shafinsa na X (Twitter), yana mai cewa: “Mutum 52 da aka daure bisa dalilan siyasa sun tsallako kan iyaka daga Belarus zuwa Lithuania lafiya.
Ya ce yana “matuƙar godiya” ga gwamnatin Amurka da Shugaba Donald Trump bisa rawar da suka taka wajen sasantawa da cimma wannan matsaya.
Daya daga cikin wadanda aka sako shi ne Mikola Statkevich, ɗan adawa mai shekaru 69 da haihuwa, wanda ya tsaya takarar shugabancin ƙasar a shekarar 2010, inda ya shafe shekaru biyar a gidan yari.
Haka zalika, Ihar Losik, ɗan jarida mai shekaru 33 daga Radio Free Europe/Radio Liberty, shi ma ya shafe shekaru biyar a tsare kafin a sako shi.
Hukumar dillancin labarai ta Belarus, Belta, ta ruwaito, cikin wadanda aka sako akwai ’yan ƙasashe 14 na waje, da suka hada da ’yan Lithuania 6, ’yan ƙasashen Latvia, Poland da Jamus biyu-biyu, sai kuma ’yan ƙasashen Faransa da Birtaniya daya-daya.
Mafi shahara cikin ’yan ƙasashen wajen da aka saki ita ce Elena Ramanauskiene, wata ’yar kasar Lithuania da aka daure a bara bisa zargin leken asiri.
Sai dai har yanzu akwai fursunoni sama da 1,000 da ke tsare kamar yadda Shugaba Nauseda ya bayyana yana mai kiran da a saki sauran fursunonin siyasa.
“Har yanzu fiye da mutum 1,000 na tsare a gidajen yari na Belarus. Dole ne mu ci gaba da ƙoƙari har sai an ba su ’yanci!”
A watan Yunin da ya gabata, Belarus ta saki wasu fursunoni siyasa 14, ciki har da Sergei Tikhanovsky, mijin Svetlana Tikhanovskaya, shugabar ’yan adawa da ke gudun hijira.
A shekarar 2020, dubban ’yan ƙasar Belarus suka gudanar da zanga-zangar ƙin amincewa da sakamakon zaɓe, wanda Lukashenko ya lashe karo na shida, lamarin da ya janyo matakin murƙushe ’yan adawa, waɗanda da dama-dama aka ɗaure su, kamar yadda ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam suka bayyana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Belarus Fursunonin Siyasa Ihar Losik
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
Aƙalla masallata 40 ’yan bindiga suka sace a wani masallaci da ke Gidan Turbe a Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara da safiyar wannan Litinin.
Majiyoyi sun ce an yi awon gaba da masallatan ne zuwa dazukan Gohori da ke yankin Tsafe.
Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a LegasWannan harin dai kai tsaye masu ruwa da tsaki na kallonsa a matsayin kawo ƙarshen yarjejeniyar sulhu tsakanin ’yan bindigar da mahukuntan jihohin Zamfara da Katsina.
A baya-bayan nan ne jihohin Katsina da Zamfara suka ƙulla yarjejeniyar sulhu tsakaninsu da ’yan bindigar da suka addabi al’ummar jihohin arewa maso yammacin Najeriyar.
Yarjejeniyar sulhu da aka cimma a dajin Wurma ta samu halartan manyan ’yan bindiga irinsu Alhaji Usman Kachalla Ruga da Muhindinge da Yahaya Sani ( Hayyu ) da kuma Shu’aibu.
A ɓangaren mahukunta, akwai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi da kuma shugaban ƙaramar hukuma Babangida Abdullahi Kurfi.
’Yan bindiga sun saki wasu mutane da suke garkuwa da su a lokacin yarjejeniyar sulhun, tare da barin al’umma zuwa gonakinsu ba tare da wata fargaba ko tsangwama.
To sai dai kuma, ƙasa da wata guda bayan cimma wannan yarjejeniya, rahotanni sun ce ’yan bindiga sun kutsawa wani ƙauye a Zamfara tare da awon gaba da masallata.
Shaidun gani da ido sun ce, maharan sun yi wa masallacin ƙawanya da misalin ƙarfe 5:30 na safe, daidai lokacin da jama’a ke sallar asuba.