Aminiya:
2025-11-02@15:25:05 GMT

INEC ta amince da jam’iyyar haɗaka ta ADC

Published: 10th, September 2025 GMT

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta amince da jam’iyyar ’yan haɗaka ta ADC, ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban Majalisar Dattawa, David Mark.

Wannan tabbaci na zuwa ne bayan hukumar ta wallafa sunayen shugabannin jam’iyyar a shafinta na intanet, abin da ya kawo ƙarshen dogon jira da aka yi tun bayan ayyana ta a matsayin jam’iyyar haɗin kan ’yan adawa a ranar 2 ga Yuli.

Masu zanga-zanga sun ƙone matar tsohon Firaministan Nepal Yadda zanga-zangar adawa da rashawa ta rikiɗe zuwa tarzoma a Nepal

Tun a watan Yulin ne dai gamayyar ’yan adawa suka ayyana David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar, tare da tsohon Gwamnan Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin sakatarenta na ƙasa.

Sai dai kafin yanzu, INEC ba ta sanya sunayensu a jerin rukunin shugabannin jam’iyyun da ta aminta da su ba a hukumance.

Sauran shugabannin da sunayensu suka bayyana a jerin da hukumar ta fitar sun haɗa da: Ibrahim Ahmad Mani  — Ma’aji, Akibu Dalhatu — Sakataren kuɗi, da kuma Oserheimen Osunbor — mai bayar da shawara kan harkokin shari’a

Gamayyar ’yan adawar a Nijeriya sun haɗe a jam’iyyar ADC ne domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a babban zaɓen 2027.

Bayan hawa kan mulki, Tinubu ya ɗauki manyan matakai da dama waɗanda suka sauya rayuwar al’ummar ƙasar, kamar cire tallafin man fetur da kuma sauye-sauye a fannin kuɗi.

A halin yanzu dai, mafi yawan manyan jam’iyyun siyasa na ƙasar na fama da rikicin cikin gida, inda suke zargin jam’iyyar APC mai mulki da yi musu zagon ƙasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Mark

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

“Amurka ba za ta tsaya kawai tana kallo ba yayin da irin waɗannan ta’addancin ke faruwa a Nijeriya da sauran ƙasashe.

“Mun shirya, muna da ƙarfi da niyyar kare Kiristoci a faɗin duniya,” in ji Trump.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano October 31, 2025 Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
  • Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
  • Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda