INEC ta amince da jam’iyyar haɗaka ta ADC
Published: 10th, September 2025 GMT
Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta amince da jam’iyyar ’yan haɗaka ta ADC, ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban Majalisar Dattawa, David Mark.
Wannan tabbaci na zuwa ne bayan hukumar ta wallafa sunayen shugabannin jam’iyyar a shafinta na intanet, abin da ya kawo ƙarshen dogon jira da aka yi tun bayan ayyana ta a matsayin jam’iyyar haɗin kan ’yan adawa a ranar 2 ga Yuli.
Tun a watan Yulin ne dai gamayyar ’yan adawa suka ayyana David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar, tare da tsohon Gwamnan Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin sakatarenta na ƙasa.
Sai dai kafin yanzu, INEC ba ta sanya sunayensu a jerin rukunin shugabannin jam’iyyun da ta aminta da su ba a hukumance.
Sauran shugabannin da sunayensu suka bayyana a jerin da hukumar ta fitar sun haɗa da: Ibrahim Ahmad Mani — Ma’aji, Akibu Dalhatu — Sakataren kuɗi, da kuma Oserheimen Osunbor — mai bayar da shawara kan harkokin shari’a
Gamayyar ’yan adawar a Nijeriya sun haɗe a jam’iyyar ADC ne domin ƙalubalantar Shugaba Bola Tinubu a babban zaɓen 2027.
Bayan hawa kan mulki, Tinubu ya ɗauki manyan matakai da dama waɗanda suka sauya rayuwar al’ummar ƙasar, kamar cire tallafin man fetur da kuma sauye-sauye a fannin kuɗi.
A halin yanzu dai, mafi yawan manyan jam’iyyun siyasa na ƙasar na fama da rikicin cikin gida, inda suke zargin jam’iyyar APC mai mulki da yi musu zagon ƙasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: David Mark
এছাড়াও পড়ুন:
Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
“Amurka ba za ta tsaya kawai tana kallo ba yayin da irin waɗannan ta’addancin ke faruwa a Nijeriya da sauran ƙasashe.
“Mun shirya, muna da ƙarfi da niyyar kare Kiristoci a faɗin duniya,” in ji Trump.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA