Kotun Ghana ta ɗaure ’yan Najeriya 3 shekaru 96 saboda satar mota
Published: 10th, September 2025 GMT
Wata kotu da ke ƙasar Ghana ta yanke wa ’yan Najeriya uku hukuncin ɗaurin shekaru 96, bayan samun su da laifin satar mota a birnin Kumasi na ƙasar.
Kotun dai ta samu Francis Friday da Linus Agwazie da kuma Russell Ekenze ne da laifin a daidai lokacin da ’yan ƙasar ke neman a kori ’yan Najeriya daga kasar saboda aikata laifuka.
Mai magana da yawun ’yan sandan yankin Ashanti na ƙasar, Godwin Ahianyo, ne ya bayyana yanke hukuncin a cikin wata sanarwa ranar Talata.
Sanarwar ta ce an kama mutanen ne ranar 20 ga watan Yuni bayan an zarge su da satar wasu motoci da ke ajiye.
Godwin ya ce bayan kama su ne aka gurfanar da su a gaban kotun a ranar 22 ga watan Yuli a gaban kotun da ke Atasemanso, kan zargin satar motar.
A ’yan watannin nan dai ana samun rahotannin ƙaruwar ’yan Najeriya da ke aikata laifuka a ƙasar ta Ghana.
Ko a watan Mayu, sai da wata kotun kasar da ke Tarkwa ta yanke wa wata ’yar Najeriya hukuncin ɗaurin shekara 20, bayan samun ta da laifin safarar ’yan mata huɗu tare da shigar da su karuwanci a ƙasar.
Kazalika, a watan Yuli, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasar ta kama ’yan Najeriya 50 bisa zargin aikata zamba ta intanet da kuma safarar mutane.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Satar mota yan Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
Mai shari’a Dahiru ya amince da buƙatar, ya kuma ɗage shari’ar zuwa ranar 12 ga watan Disamba, 2025, domin ci gaba da sauraron shari’ar.
Ƙuli-ƙuli dai nau’in abin ci ne mai taushi da ake yi da gyaɗa, ana soyawa har sai ya zama ƙura-ƙura ta yadda za a ci cikin nishaɗi.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA