Aminiya:
2025-11-02@21:10:39 GMT

Kotun Ghana ta ɗaure ’yan Najeriya 3 shekaru 96 saboda satar mota

Published: 10th, September 2025 GMT

Wata kotu da ke ƙasar Ghana ta yanke wa ’yan Najeriya uku hukuncin ɗaurin shekaru 96, bayan samun su da laifin satar mota a birnin Kumasi na ƙasar.

Kotun dai ta samu Francis Friday da Linus Agwazie da kuma Russell Ekenze ne da laifin a daidai lokacin da ’yan ƙasar ke neman a kori ’yan Najeriya daga kasar saboda aikata laifuka.

Injin niƙa ya yi ajalin matar aure mai ’ya’ya 6 a Gombe Mamakon ruwan sama ya hallaka mutum 3 a Zariya

Mai magana da yawun ’yan sandan yankin Ashanti na ƙasar, Godwin Ahianyo, ne ya bayyana yanke hukuncin a cikin wata sanarwa ranar Talata.

Sanarwar ta ce an kama mutanen ne ranar 20 ga watan Yuni bayan an zarge su da satar wasu motoci da ke ajiye.

Godwin ya ce bayan kama su ne aka gurfanar da su a gaban kotun a ranar 22 ga watan Yuli a gaban kotun da ke Atasemanso, kan zargin satar motar.

A ’yan watannin nan dai ana samun rahotannin ƙaruwar ’yan Najeriya da ke aikata laifuka a ƙasar ta Ghana.

Ko a watan Mayu, sai da wata kotun kasar da ke Tarkwa ta yanke wa wata ’yar Najeriya hukuncin ɗaurin shekara 20, bayan samun ta da laifin safarar ’yan mata huɗu tare da shigar da su karuwanci a ƙasar.

Kazalika, a watan Yuli, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasar ta kama ’yan Najeriya 50 bisa zargin aikata zamba ta intanet da kuma safarar mutane.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Satar mota yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Mai shari’a Dahiru ya amince da buƙatar, ya kuma ɗage shari’ar zuwa ranar 12 ga watan Disamba, 2025, domin ci gaba da sauraron shari’ar.

Ƙuli-ƙuli dai nau’in abin ci ne mai taushi da ake yi da gyaɗa, ana soyawa har sai ya zama ƙura-ƙura ta yadda za a ci cikin nishaɗi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure