Kotun Ghana ta ɗaure ’yan Najeriya 3 shekaru 96 saboda satar mota
Published: 10th, September 2025 GMT
Wata kotu da ke ƙasar Ghana ta yanke wa ’yan Najeriya uku hukuncin ɗaurin shekaru 96, bayan samun su da laifin satar mota a birnin Kumasi na ƙasar.
Kotun dai ta samu Francis Friday da Linus Agwazie da kuma Russell Ekenze ne da laifin a daidai lokacin da ’yan ƙasar ke neman a kori ’yan Najeriya daga kasar saboda aikata laifuka.
Mai magana da yawun ’yan sandan yankin Ashanti na ƙasar, Godwin Ahianyo, ne ya bayyana yanke hukuncin a cikin wata sanarwa ranar Talata.
Sanarwar ta ce an kama mutanen ne ranar 20 ga watan Yuni bayan an zarge su da satar wasu motoci da ke ajiye.
Godwin ya ce bayan kama su ne aka gurfanar da su a gaban kotun a ranar 22 ga watan Yuli a gaban kotun da ke Atasemanso, kan zargin satar motar.
A ’yan watannin nan dai ana samun rahotannin ƙaruwar ’yan Najeriya da ke aikata laifuka a ƙasar ta Ghana.
Ko a watan Mayu, sai da wata kotun kasar da ke Tarkwa ta yanke wa wata ’yar Najeriya hukuncin ɗaurin shekara 20, bayan samun ta da laifin safarar ’yan mata huɗu tare da shigar da su karuwanci a ƙasar.
Kazalika, a watan Yuli, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasar ta kama ’yan Najeriya 50 bisa zargin aikata zamba ta intanet da kuma safarar mutane.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Satar mota yan Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
A ƙalla fasinjoji 17 ne suka rasa rayukansu bayan wata motar haya ta faɗa cikin wata gada da ta ruguje a kan titin Gwalli da ke ƙaramar hukumar Gummi, jihar Zamfara.
A cewar hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa (FRSC) reshen Zamfara, hatsarin ya faru ne a daren Lahadi lokacin da motar ɗauke da kaya da fasinjoji ta faɗa cikin gadar da ta ruguje. Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, SRC Isah Aliyu, ya tabbatar da lamarin a wata sanarwa da ya fitar.
Kwamandan FRSC na jihar, CC Aliyu Magaji, wanda ya ziyarci wurin hatsarin, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa da asarar rayukan, inda mafi yawansu mata ne. Ya ce hatsarin ya biyo bayan nauyin da aka ɗora wa motar fiye da ƙima da kuma tafiya da daddare.
Hukumar ta gode wa mazauna yankin da suka gaggauta taimakawa wajen ceto wasu daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su. Kwamanda Aliyu ya yi ta’aziyya ga gwamnatin Zamfara da al’ummar Gummi, tare da yin kira ga direbobi su rika bin ƙa’idojin hanya da kuma guje wa tuƙa mota da dare domin kare rayuka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp