Aminiya:
2025-11-02@21:51:13 GMT

An ceto ɗan ƙasar Masar da aka yi garkuwa da shi a Oyo

Published: 10th, September 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Oyo ta sanar da ceto wani ɗan ƙasar Masar da wasu da ba a san ko su wane ba suka yi garkuwa da shi.

Kakakin rundunar, CSP Adewale Osifeso, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Talatar nan a Ibadan, babban birnin jihar.

DSS ta warware tankiyar da ke tsakanin NUPENG da Dangote ’Yan bindiga sanye da hijabi sun sace mutane 11 a Zamfara

Ya ce an ceto ɗan Masar ɗin ne a ranar Talata da safe — kwana ɗaya kacal bayan sace shi — ba tare da an biya kuɗin fansa ba.

Osifeso ya ce an sace mutumin ne a yankin Alomaja, kusa da garin Idi-Ayunre, wani yanki da ke gefen birnin Ibadan.

A cewarsa, bayan samun rahoton garkuwar, sai Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Oyo, CP Femi Haruna, ya bayar da umarnin gaggawa ga sashen yaki da masu garkuwa da mutane na rundunar.

Hakan ce ta sanya sashen ya haɗa gwiwa da rundunar ’yan sanda ta Jihar Ogun da kuma wasu mafarauta, inda suka shiga dazukan da ke tsakanin jihohin Oyo da Ogun domin kai farmaki.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, an yi saar gaske yayin da cikin awa 24 kacal, jami’an suka ceto ɗan ƙasar Masar daga hannun masu garkuwar.

Kakakin ’yan sandan ya ƙara da cewa yanzu haka an kai mutumin Asibitin Rundunar ’Yan Sanda na Eleyele da ke Ibadan domin duba lafiyarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Oyo Masar

এছাড়াও পড়ুন:

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Dan wasan da ya lashe kyautar a bara, Ademola Lookman na Nijeriya ba ya cikin jerin ‘yan wasan da aka lissafo a bana, inda hukumar kwallon kafa ta Afirka (Caf) ta samar da kwamitin kwararru wanda ya zakulo masu horarwa da ‘yan wasan da suka “Taka rawar gani” a tsakanin 6 ga watan Janairu zuwa 15 ga watan Oktoban wannan shekara.

An bayyana sunan mai horar da tawagar ‘yan kwallon kafa ta kasar Cape Berde, Bubista a matsayin mai neman lashe kyautar mai horarwa mafi kwazo bayan jagorantar tawagar kasar ta Blue Sharks wajen samnun gurbin gasar kofin duniya a karon farko a tarihi.

Haka nan tawagar ta tsibirin Cape Berde na cikin masu gogayyar lashe kungiya mafi hazaka a shekarar, tare da Morocco wadda a baya-bayan nan ta lashe kofin duniya na gasar kwallon kafa ta ‘yan kasa da shekara 20.

‘Yanwasa mata na Nijeriya Esther Okoronkwo da Rasheedat Ajibade na cikin wadanda ke neman lashe kyautar zakarun ‘yanwasa mata na Afirka na wannan shekarar. Ya zuwa yanzu dai hukumar CAF ba ta bayyana ranar da za a yi bikin bayar da kyautar ba.

Dan wasa mafi Kwazo: Andre-Frank Zambo Anguissa (Napoli da Kamaru), Denis Bouanga (Los Angeles FC da Gabon), Serhou Guirassy (Borussia Dortmund da Guinea), Achraf Hakimi (Paris St-Germain da Moroko), Oussama Lamlioui (Renaissance Berkane), Fiston Mayele (Pyramids da DR Congo), Iliman Ndiaye (Eberton da Senegal), Bictor Osimhen (Galatasaray da

Nigeria), Mohamed Salah (Liberpool da Masar), Pape Matar Sarr (Tottenham Hotspur da Senegal).

Mai tsaron raga na maza: Yassine Bounou (Al Hilal da Moroko), Aymen Dahmen (CS Sfadien da Tunisia), Marc Diouf (TP Mazembe da Senegal), Edouard Mendy (Al-Ahli da Senegal), Munir Mohamedi (RS Berkane da Moroko), Stanley Nwabali (Chippa Utd da Nijeriya), Andre Onana

(Trabzonspor da Kamaru), Ahmed El Shenawy (Pyramids da Masar), Bozinha (Chabes da Cape Berde), Ronwen Williams (Mamelodi Sundowns da Afirka ta Kudu).

Mai horar da kungiyar maza: Bubista (Cape Berde), Moine Chaabani (Renaissance Berkane), Hossam Hassan (Masar), Krunoslab Jurcic (Pyramids), Mohamed Ouahbi (Moroko U20), Romuald Rakotondrabe (Madagascar), Walid Regragui (Moroko), Tarik Sektioui (Moroko U23), Pape Thiaw (Senegal), Sami Trabelsi (Tunisia).

Tawagar maza: Algeria, Cape Berde, Masar, Ghana, Ibory Coast, Moroko, Moroko U20, Senegal, Afirka ta Kudu, Tunisia. ‘Yan wasa Mata da ke takarar lashe zakarun Afirka na shekara ta 2025.

‘Yar wasa mafi kwazo: Rasheedat Ajibade (Paris St-Germain da Nijeriya), Barbra Banda (Orlando Pride da Zambia), Portia Boakye (Hapoel Petah Tikba da Ghana), Tabitha Chawinga (Lyon da Malawi), Temwa Chawinga (Kansas City da Malawi), Ghizlaine Chebbak (Al Hilal da Moroko), Mama Diop (Strasbourg da Senegal), Rachael Kundananji (Bay FC da Zambia),

Sanaa Mssoudy (AS FAR da Moroko), Esther Okoronkwo (AFC Toronto da

Nijeriya).

Mai tsaron raga na mace: Sedilame Boseja (Mamelodi Sundowns da Botswana), Andile Dlamini (Mamelodi Sundowns da Afirka ta Kudu), Habiba Emad (FC Masar da Masar), Khadija Er-Rmichi (AS FAR da Moroko), Fatoumata Karantao (MUSFAS Bamako da Mali), Cynthia Konlan (Swieki United da Ghana), Adji Ndiaye (AS Bambey da Senegal), Fideline Ndoy (TP

Mazembe da DR Congo), Chloe N’Gazi (Marseille da Algeria), Chiamaka Nnadozie (Brighton & Hobe Albion da Nijeriya).

Mai horar da kungiyar mata: Genobeba Anonman (15 de Agosto), Kim Bjorkegren (Ghana), Lamia Boumehdi (TP Mazembe), Desiree Ellis (Afirka ta Kudu), Carol Kanyemba (Zambia U17), Adelaide Koudougnon (Ibory Coast U17), Justin Madugu (Nijeriya), Bankole Olowookere (Nijeriya U17), Siaka Gigi Traore (ASEC Mimosas), Jorge Bilda (Moroko).

Tawagar mata: Kamaru U17, Ghana, Ibory Coast U17, Mali, Morocco, Nijeriya, Nijeriya U17, Afirka ta Kudu, Tanzania, Zambia U17. Za ku iya ganin cikakken jerin wadanda ke neman lashe kyautukan a shafin hukuma Caf. [1]

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025 Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025 Wasanni El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid October 26, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m