Aminiya:
2025-09-17@23:13:16 GMT

An ceto ɗan ƙasar Masar da aka yi garkuwa da shi a Oyo

Published: 10th, September 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Oyo ta sanar da ceto wani ɗan ƙasar Masar da wasu da ba a san ko su wane ba suka yi garkuwa da shi.

Kakakin rundunar, CSP Adewale Osifeso, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Talatar nan a Ibadan, babban birnin jihar.

DSS ta warware tankiyar da ke tsakanin NUPENG da Dangote ’Yan bindiga sanye da hijabi sun sace mutane 11 a Zamfara

Ya ce an ceto ɗan Masar ɗin ne a ranar Talata da safe — kwana ɗaya kacal bayan sace shi — ba tare da an biya kuɗin fansa ba.

Osifeso ya ce an sace mutumin ne a yankin Alomaja, kusa da garin Idi-Ayunre, wani yanki da ke gefen birnin Ibadan.

A cewarsa, bayan samun rahoton garkuwar, sai Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Oyo, CP Femi Haruna, ya bayar da umarnin gaggawa ga sashen yaki da masu garkuwa da mutane na rundunar.

Hakan ce ta sanya sashen ya haɗa gwiwa da rundunar ’yan sanda ta Jihar Ogun da kuma wasu mafarauta, inda suka shiga dazukan da ke tsakanin jihohin Oyo da Ogun domin kai farmaki.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, an yi saar gaske yayin da cikin awa 24 kacal, jami’an suka ceto ɗan ƙasar Masar daga hannun masu garkuwar.

Kakakin ’yan sandan ya ƙara da cewa yanzu haka an kai mutumin Asibitin Rundunar ’Yan Sanda na Eleyele da ke Ibadan domin duba lafiyarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Oyo Masar

এছাড়াও পড়ুন:

Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS

Hukumar ƙididdigar a Najeriya NBS ta bayyana cewa an samu raguwar hauhawar farashin kaya a watan Agusta idan aka kwatanta da watan Yulin da ya gabace shi.

Cikin sabbin alƙaluman da NBS ta fitar a ranar Litinin sun nuna cewa an samu raguwar kashi 1.76 a watan Agustan saɓanin watan Yulin, wanda ya nuna karo na hudu ke nan a jere hauhawar farashin yana sauka.

NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murna

Rahoton na hukumar NBS na zuwa ne kwanaki bayan da Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin karya farashin kayan abinci ƙasar.

A watanin baya-bayan an riƙa samun raguwar hauhawar farashin kayyaki a ƙasar.

Ko alƙaluman da NBS ta fitar a watan Yuni, ta bayyana cewa hauhawar farashi a Najeriya ya sauka zuwa kashi 22.22 daga 22.97 da aka samu a watan Mayu.

A baya dai dai an yi ta kiraye-kirayen gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakan rage hauhawarar farashi domin magance tsadar rayuwa da ake fuskanta a ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya