Aminiya:
2025-11-02@16:54:54 GMT

MDD ta buƙaci hukumomin Najeriya su kamo waɗanda suka kai hari a Bama

Published: 8th, September 2025 GMT

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi Allah-wadai da harin da ’yan ta’adda suka kai a garin Darul Jamal, da ke yankin Bama na Jihar Borno.

Harin wanda ya faru a yammacin ranar Juma’a 5 ga watan Satumba ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 60 tare da sace wasu da dama ciki har da sojoji da fararen hula.

A wata sanarwa da Mohamed Malick Fall, babban jami’i mai kula da ayyukan jinƙai na Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya ya fitar, ya bayyana matukar bakin cikinsa kan lamarin.

MDD ta yi kira ga hukumomin Najeriya da su gano waɗanda suka kai wannan harin tare da ɗaukar mataki a kansu.

Fall ya ce: “Ina kira ga hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aikin. Ina kuma kira da a gaggauta ceto duk waɗanda aka sace.”

Yarima Harry ya ziyarci kabarin Sarauniya Elizabeth II Matatar Dangote ta musanta dakatar da aiki

“Ina matuƙar baƙin ciki da rahoton kisan da aka yi wa sojoji da fararen hula da dama a ranar Juma’a a ƙauyen Darajamal da ke ƙaramar hukumar Bama a Jihar Borno da ke Arewa maso Gabashin Najeriya”

A madadin Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya, Fall ya miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ya shafa, gwamnati, da kuma al’ummar Jihar Borno, tare da yi wa waɗanda suka ji rauni fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

Rahotannin sun ce an kashe fararen hula fiye da 60, inda ake zargin an yi garkuwa da waɗanda ba a san adadinsu ba.

Wasu da dama sun tsere, kuma gidaje fiye da 20 sun ƙone ƙurmus a harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Harin Bama Harin boko haram waɗanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi

’Yan bindiga sun sace Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Honarabul Samaila Bagudu, a garinsu da ke Ƙaramar Hukumar Bagudu.

Rahotanni sun bayyana cewa ’yan bindigar sun mamaye garin Bagudu ne da yammacin ranar Juma’a tare da yin harbe-harbe don tsorata al’umma.

Maharan sun yi awon gaba da ɗan majalisar ne a kan hanyarsa ta dawowa daga masallaci bayan ya an idar da sallah masallaci a garin na Bagudu.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnatin Jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya ce an sanar da hukumomin tsaro, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da kuɓutar da Mataimakin Shugaban Majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari