Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana
Published: 8th, September 2025 GMT
Saboda tsabar gudunsu da kuma zilliya inda suke da sauri ninki biyar na gudun sauti makamai ne da ka iya sauya yadda ake fafata yaki a yanzu.
Hakan ta sa yanzu kasashe ke rige-rigen samar da su.
Rasha, China, Amurka: rigegeniyar nuna iko Bikin faretin na Beijing ya jawo rade-radi game da barazanar da China ke yi wa kasashen Yamma da makamanta masu linzami.
Amurka kuma, na kokarin kamo su ne, yayin da Birtaniya kuma ba ta da su.
William Freer, wani mai nazarin harkokin tsaro a cibiyar Council on Geostrategy, na ganin dalilin da ya sa Rasha da China suka zarce saura abu ne mai sauki.
“Sun yanke shawarar zuba kudade masu yawa a wadannan fannonin tun shekaru baya.”
A gefe guda kuma, kasashen Yamma sun fi mayar da hankali tun daga shekara 20 da suka wuce wajen yaki da masu ikirarin jihadi a gida da kuma kasashen waje.
A lokacin, yiwuwar gwabza yaki tsakanin manyan kasashe masu karfin soji iri daya ba ta da yawa.
Aikin gwajin wani makami mai linzami mai matsakaicin nisa a Koriya ta Arewa
“Abin da ya faru shi ne, mun gaza wajen lura da barazanar China wajen inganta rundunar sojinta,” kamar yadda Sir Aled Younger, wanda ya bar mukamin shugaban hukumar tattara bayanan sirri ta Birtaniya a 2020, ya bayyana.
Sauran kasashe na ta kokari su ma: Isra’ila na da makamin hypersonic mai suna Arrow 3 wanda aka kirkira domin kakkabo makamai.
Iran ta yi ikirarin cewa tana da shi, wanda ta ce ta harba wa Isra’ila lokacin yakin kwana 12 da suka gwabza a watan Yuni.
(Tabbas makamin ya yi gudun walkiya amma ba a tunanin yana da ikon zilliya mai yawa da za a kira shi cikakken hypersonic).
Koriya ta Arewa ma na ta yin aiki kan nata tun 2021, har ma ta yi ikirarin cewa tana da makamin.
Yanzu Amurka da Birtaniya na zuba kudade a fannin makaman hypersonic, kamar yadda saura kamar Japan da Faransa ke yi.
Amurka ta kaddamar da nata makamin mai gudun hypersonic mai suna “Dark Eagle”.
Amma dai a yanzu China da Rasha ne kan gaba sosai, inda wasu masana a kasashen Yamma ke cewa abin damuwa ne.
Dankaren gudu da mummunar barna
Kalmar hypersonic na nufin wani abu mai gudun tsiya kan ma’aunin March 5 ko sama da haka. Ma’ana mai gudu ninki biyar na sauti ko kuma gudun mil 3,858 cikin awa daya.
Wannan gudun nasu shi ne abin da ya sa ake fargaba game da su.
Makamin da aka sani mafi gudu zuwa yanzu shi ne na Rasha mai suna Abangard – wanda aka ce ya kan yi gudun Mach 27 (kusan mil 20,700 cikin awa daya), kodayake an fi ambato gudun Mach 12.
Game da barnar da suke haifarwa, irin wadannan makaman ba su fi sauran makamai masu linzami hadari mai yawa ba, a cewar Mista Freer.
“Wahalar ganowa da kuma kakkabo su ce ke sakawa ana tsoronsu sosai.”
Akan harba su ne da taimakon wata roka, idan suka kai kololuwar tashi sai kuma su shiga wani yanayi da ake kira “scramjet engine” wanda shi kuma zai yi musu jagora domin dira inda aka aika su.
Akan yi amfani da su ta hanya biyu, ma’ana bam din suke dauke da shi zai iya zama na nukiliya ko kuma gama-garin bam.
Kafin a ayyana makami a matsayin mai gudun walkiya na hypersonic, dole ne sai ya mallaki ikon zillewa makaman kariya. Wanda ya harba shi zai dinga sassauya masa hanyar tafiya ta yadda abokin gabarsa ba zai iya gane shi ba har sai ya dira kan wurin da ya nufa.
“Ta hanyar kauce wa nau’rorin leken samaniya, sukan kauce wa abokan gaba har sai lokacin da suke dab da isa wanda hakan zai sa babu damar da za a iya tare su,” Patrycja Bazylczyk, mai bincike a sashen Missile Defence Project na cibiyar Centre for Strategic and International Studies da ke Amurka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Rasha
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani
Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.
Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci