Ambaliyar Ruwa: NEMA ta ceto mata 2 da jaririya a Kaduna
Published: 7th, September 2025 GMT
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ta ce ta samu nasarar ceto wasu mata biyu da wata jaririya da ambaliyar ruwa ta rutsa da su a Jihar Kaduna.
Shugabar hukumar, Hajiya Zubaida Umar ce, ta bayyana hakan a shafinta na Facebook.
Harin Boko Haram: Zulum ya kai ziyarar jaje garin Darajamal Tsadar Rayuwa: NLC ta buƙaci gwamnati ta sake duba albashin ma’aikataTa ce ambaliyar ta auku ne sakamakon ruwan sama mai yawa da aka yi a ranar Juma’a.
Ta ce sama da gidaje 160 da magidanta 500 ne ambaliyar ta shafa a unguwanni irin su Kabala Doki, Bachama, Kigo, Ramat, da Unguwar Dosa/Nasarawa/Mali.
Rahoton ya nuna cewa ruwan kogin Kaduna ne ya yi sama, ya shiga unguwanni, lamarin da ya haddasa ambaliyar.
Shugaban NEMA na Kaduna, Malam Suleiman Mohammed, ne ya jagoranci aikin ceto tare da haɗin gwiwar hukumomin agaji na jihar.
NEMA, ta ce za ta ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin agaji domin tallafa wa waɗanda ambaliyar ta shafa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Jaririy
এছাড়াও পড়ুন:
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.
An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.
Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.
An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.
Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.
Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp