Aminiya:
2025-11-02@03:54:56 GMT

Tsadar Rayuwa: NLC ta buƙaci gwamnati ta sake duba albashin ma’aikata

Published: 7th, September 2025 GMT

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) da ma’aikatan gwamnati, sun buƙaci Gwamnatin Tarayya, ta sake duba mafi ƙarancin albashi, domin Naira Naira 70,000 da ake biya yanzu ba ta isa wajen tafiyar da al’amuran yau da kullum.

A cewarsu tashin farashin kayan abinci, sufuri, haya, da wutar lantarki ya ƙara jefa su cikin wahalar da rayuwa.

Sojoji sun bankaɗo mafakar ’yan ta’adda da makamai a Taraba Najeriya ce ƙasa ta biyar mafi yawan Musulmai a duniya

A wasu jihohi kamar Imo, Legas da Ribas sun riga sun ƙara mafi ƙarancin albashi sama da wanda gwamnatin tarayya ke biya.

Mista Benson Upah, Sakataren riƙo na NLC, ya ce: “Naira 70,000 ba za ta iya ɗaukar nauyin rayuwa a wannan yanayi na tattalin arziƙi da ake ciki ba.

“Ma’aikata na cikin matsin lamba sosai, kuma idan gwamnati ba ta ɗauki mataki cikin gaggawa ba, matsalar rayuwa za ta ƙara tsananta.”

Shi ma shugaban ƙungiyar manyan ma’aikata, Mista Shehu Mohammed, ya jaddada buƙatar ɗaukar mataki cikin gaggawa.

“Idan mutum ya biya kuɗin wuta daga Naira 70,000, abin da ya rage ba zai iya ciyar da iyalinsa har tsawon kwana goma ba. Gwamnatin Tarayya dole ta yi saurin ɗaukar mataki.”

Ma’aikata na buƙatar gwamnati ta ƙara albashi tare da aiwatar da manufofin da za su rage tsadar rayuwa a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Mafi ƙarancin albashi tsadar rayuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.

Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Trump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.

A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”

A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.

“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.

“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”

Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.

“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.

Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • Kamfanin Amazon na shirin sallamar ma’aikata 600,000 don maye gurbinsu da mutum-mutumi
  • Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya
  • Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati