Hajiya Sa’ah ta kuma bayyana cewa ita wannan ƙidaya da yin rajistar haihuwa, aure da sauran su, abubuwa ne masu muhimmanci da za su taimaka wa gwamnati ta san yawan su, ta yadda za su sami nasarar ci gaba da lasar romon Dimokraɗiyya mai yawa, musamman a bangaren ilmi, lafiya da dai sauran abubuwan more rayuwa.

 

Daga nan ne ta jinjina wa Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani da cewar jihar Kaduna ce jiha ta farko da gwamnan ta ya yi yunƙurin gabatar da wayar da kan al’ummar sa game da muhimmancin ƙidaya, kuma lallai yana bayar da cikakken goyon bayan sa a kan haka, inda ya ɗauki nauyin hakan a dukkan Ƙananan Hukumomin jihar.

 

A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Sabon Gari, Malam Jamilu Abubakar Albani (ALGON), wanda ya samu wakilcin mataimakin sa, ya bayyana cewa su a shirye suke su bayar da dukkan goyon bayan da ake nema.

 

Ya ce, su tun a baya sun fara wayar ma al’ummar Ƙaramar Hukumar su kai game da manufa da muhimmancin shirin ƙidayar a gare su. Sun shiga lungu da saƙo don wayar ma da al’ummar su kai game da shirin ƙidayar da ke tunkarowa, wanda zai gudana nan ba da jimawa ba.

 

Ɗaya daga cikin Malaman addinai da suka halarci taron ya tabbatar da ƙidayar al’umma a cikin tsarin addinin musulunci, domin shi ne yake bada damar sanin tsatson dukkan ɗan adam da kuma tabbatar da rayuwa cikin tsari.

 

Shi ma a nasa jawabin, wani Shugaba a addinin kirista ya nuna farin cikin sa, sannan kuma nuna yadda zasu wayar ma da mabiyan su kai game da ƙidayar. Ya kuma ƙara da ceawar a koyaushe hukumar ƙidayar suka shirya, su ma a shirye suke wajen ganin an cimma gaci.

 

A looacin da tawagar Kwamishiyar ta isa Ƙaramar Hukumar Soba, Shygaban Ƙaramar Hukumar, Hon. Muhammad Shehu Lawal Molash, ya bayyana jin daɗin sa da wannan shiri na ƙidaya, inda ya nuna cewa za su bayar da duk gudumawa da haɗin kan da ake nema don samun nasarar aikin.

 

Shi kuwa Sarki Haladu, jan hankalin matasa ya yi da su kauce ma duk wata hayaniya, su zama masu natsuwa tun a yanzu wajen wayar ma da al’umma kai har zuwa kammala shirin.

 

Ya zuwa haɗa wannan rahoton dai, Kwamishiniya Hajiya Sa’adatu Dogon Bauchi tana ci gaba da zagawa zuwa sauran Ƙananan Hukumomin jihar don ƙara wayar da kan jama’a game da muhimmancin wannan ƙidaya da ke tafe.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ƙaramar Hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

A cewarsa, ta hanyar wadannan shirye-shirye, kasar Sin ta nuna goyon baya mai dorewa ga kasashe masu tasowa kuma tana ba da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban duniya a karkashin tsarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher