Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Published: 6th, September 2025 GMT
Ya kara da cewa, saboda haka; akwai bukatar a kara yawan hektar noman kwakwar manjar zuwa hekta akalla 500,000, domin cike gibin bukatar da ake da ita a kasar nan tare kuma da kara bunkasa nomanta a Nijeriya baki-daya.
Shugaban ya ci gaba da cewa, har yanzu a Nijeriya ana ci gaba da fuskantar samun gibi wajen samar da kwakwar, sai dai ya bayyana cewa; sama da shekara 10 zuwa shekara 15 kungiyar ta POFON ta yi namijin kokari, wajen kara yawan noman kwakwar a daukacin fadin kasar.
A cewarsa, manyan gonaki a kasar da ke nomanta kamar irin su, Presco da kuma Okomu sun kara dage damtse wajen zuba hannun jari da kuma kara fadada gonakin noman kwakwar manjan kwarai da gaske.
Haka zalika, shugaban ya bayyana cewa; wasu sabbin gonaki kamar irin su Dufil, Saro Africa da sauransu, sun shiga Jihar Edo tare da zuba hannun jari a fannin na noman kwakwar.
“Saro Africa, ta samar da hekta 20,000 a Jihar Edo, Wilmar ta mallaki hektar noman kwakwar ta PZ Wilmar, inda yanzu yake kokarin sake noma wasu hektocin guda 8,500, wanda hakan zai bai wa gonar damar hekta guda 50,000 a cikin kasar.
“Gonakin JB, su ma sun kara zuba hannun jarinsu a Jihar Kuros Ribas, inda a yanzu suke kan kara samar da wasu hekta guda 10,000, ta noman kwakwar manjan a Jihar Ondo,” a cewar shugaban.
Ya ci gaba da cewa, akwai kuma wata gonar ta noman kwakwar manjan da ke ci gaba da kara zuba hannun jarinsu.
“Kimanin shekaru takwas da suka gabata, jimillar gundarin manjan da ake samarwa a kasar, a wannan yankin ake samar da shi wanda ya kai daga tan 900,000 zuwa tan miliyan daya,“ in ji shugaban.
“Ya zuwa yanzu, mun samu nasarar kara yawansa zuwa kimanin daga miliyan 1.4 zuwa miliyan 1.5, wanda hakan ya nuna cewa; ya kai kashi 50 na manjan da aka sarrafa,” in ji Ibru.
Koda-yake dai, shugaban ya sanar da cewa; ana ci gaba da samun gibi a samar da kwakwar manjan a kasar, amma kungiyar na kan yin aiki da wasu hukumomin gwamnati, domin samar da wani jadawalin kara bunkasa fannin a kasar nan da kuma kara zuba kudi a bangaren.
Ya yi nuni da cewa, jadawalin, ba wai kawai manyan masu noman kwakwar manjan ba ne, hatta su ma kananan monoma a fannin, za su yi matukar amfana.
Da yake yin tsokaci kan tsadar manjan a fadin wannan kasa, Ibru ya bayyana cewa; kungiyar na ci gaba da yin kokari wajen daidaita farashinsa kwarai da gaske.
“A wannan kasa da muke ciki, sau biyu ake yin noman kwakwar manja a shekara, yadda idan aka girbe ta da yawa, farashin nata ke raguwa daga baya kuma farashin ya kara tashi,“ a cewar shugaban.
Haka zalika, ya sanar da cewa; ‘ya’yan kungiyarmu na matukar kokari wajen ganin sun daidata farashin manjan a fadin kasar baki-daya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: noman kwakwar manjan
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.
A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.
Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFAYana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.
“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”
“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.
“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”
“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.