An haramta wa makarantu tilasta wa iyaye sayen sabbin litattafai duk shekara a Filato
Published: 6th, September 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Filato, ta haramta wa makarantu a jihar tilasta iyayen ɗalibai sayen sabbin littattafai duk shekara.
Wannan mataki ya biyo bayan ƙudurin da Hon. Joseph Bukar, ɗan majalisa mai wakiltar Shendam ya gabatar, tare da goyon bayan Hon. Mathew Kwarpo Sylvanus daga Mangu ta Kudu.
Sarkin Zazzau ya jagoranci jama’a domin murnar Maulidin bana Gwamnatin Sakkwato ta bai wa ’yan gudun hijira tallafin kuɗi da shinkafaBukar, ya ce bai dace ba a ci gaba da tilasta wa iyaye siyan sabbin littattafai duk shekara, inda ya ce hakan cin zarafi ne.
’Yan majalisar sun ce wannan mataki zai rage wa iyaye nauyin kashe kudi.
Sun bayyana cewa ana iya sake amfani da littattafai, har ma a raba wa ’yan uwa da abokan arziƙi.
Majalisar ta amince da cewa:
1. Iyaye su samu ’yancin sayen littattafai daga ko ina, ba dole sai a makarantu ba.
2. An riƙa amfani da littattafai aƙalla shekaru huɗu, kamar yadda ake yi a jihohin Edo da Imo.
3. Makarantu da ƙungiyoyin iyayen ɗalibai su kafa bankin littattafai da tsarin musayar littattafai domin rage kashe kuɗi.
Majalisar ta kuma yi Allah-wadai da al’adar yin bikin kammala makaranta a matakin firamare da ajin ’yan yara.
Ta bayyana cewa hakan ɓata lokaci da kuɗi ne, kuma ba shi da amfani ga ilimi.
Domin tabbatar da bin dokar, majalisar ta umarci kwamitin ilimi da ya kira shugabannin makarantu masu zaman kansu tare da jami’an ma’aikatar ilimi, don sanar da wannan matsaya.
An kuma gargaɗi makarantu cewa duk wanda ya saɓa wa wannan umarni za a hukunta shi.
Hakazalika, majalisar ta tattauna kan matsalar dillalan gidaje waɗanda ba su lasisi.
’Yan majalisar sun koka da yadda ake cutar da jama’a ta hanyar tatsarsu maƙudan kuɗaɗe.
Don haka, an amince da haramta ayyukan dillalai waɗanda ba su da lasisi tare da samar da sabon tsari domin maye gurbin tsohuwar dokar haya.
Kakakin majalisar, Rt. Hon. Naanlong Daniel, ya yaba wa ’yan majalisar bisa gudunmawarsu, tare da tabbatar da cewa majalisar za ta ci gaba da samar da dokoki da za su kawo sauƙi da ci gaban al’ummar Filato.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai iyaye Majalisar Dokoki makarantu majalisar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa ya bukaci ma’aikatar kananan hukumomi da ta karfafa matakan yiwa kananan hukumomin jihar 27 jagoranci akan sha’anin mulki da harkokin kudi domin inganta ayyukan su.
Shugaban Kwamatin, Alhaji Aminu Zakari ya yi wannan kiran a karshen ziyarar kwanaki 3 da kwamatin ya yi a ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar a Dutse.
Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa a majalisar dokokin jihar Jigawa, ya ce ziyarar kwamatin na da nufin tantance yadda ma’aikatar ta ke gudanar da ayyukan ta, ta fuskar harkokin mulki da na kudi da kuma dangantakar aiki tsakanin ta da kananan hukumomin jihar 27 kamar yadda tsarin mulki ya dorawa majalisa nauyi.
A nasa jawabin, mataimakin shugaban Kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama, Alhaji Sani Sale Zaburan ya bayyana bukatar ganin jami’an ma’aikatar da ke kula da kananan hukumomi a shiyya shiyya suna gudanar da ayyukan su ba tare da jingina da shugabannin kananan hukumomi ba a ko da yaushe amma Kuma su na yiwa kananan hukumomin jagoranci wajen gudanar da sha’anin mulki da harkokin Kudi kamar yadda ya kamata.
Daya daga cikin ‘yan kwamatin Malam Ibrahim Sabo Ahmad Roni ya duba kundin bayanan sha’anin mulki yayin da Oditoci su ka duba kundin bayanan harkokin Kudi tare da yabawa da kuma bada shawarwari da za su inganta ayyukan ma’aikatar.
Da ya ke mayar da jawabi, kwamishinan ma’aikatar kananan hukumomi Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa wanda Babban Sakatare na maikatar ya wakilce shi, Alhaji Muhammad Yusha’u ya ce ma’aikatar ce ke uwa da makarbiya wajen yiwa kananan hukumomi jagoranci a sha’anin mulki da harkokin Kudi da zamantakewa domin kawo cigaba a yankunan karkara.
Kazalika, a daya bangaren kuma, karamin Kwamatin da Babban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa ya kafa bisa jagorancin wakilin mazabar Kiyawa Alhaji Yahaya Muhammad Andaza domin duba aikin gyaran gidajen kananan hukumomin jihar 27 da ke kan titin Bypass a Dutse ya mika rahoton sa ga babban kwamatin.
Alhaji Yahaya Muhammad Andaza Wanda sakataren Kwamatin Alhaji Yusha’u Muhammad ya wakilta, ya ce karamin Kwamatin ya duba gidajen Inda ya dauki samfur din yanayin da su ke ciki.
Ya ce daga cikin gidajen akwai wadda ke funskatar matsaloli kamar na tsagewar bango da sanya darduma da kujeru da kayan amfani a dakin girki marasa inganci yayin da ba a mayar da na’urar sanyaya daki a wasu gidajen ba.
Yusha’u wanda shi ne mataimakin Akawun majalisar, ya lura cewa akwai rashin kyawun flasta a wasu gidajen yayin da kan dakin wasu ke yayyo sai Kuma rashin fankar sama da karayyayun kujeru da rashin hada wasu gidajen da wutar lantarki mai amfani da hasken rana da rashin kyawun kofofi da magudanin ruwa da ke kawo barazanar ambaliyar ruwa ga wasu gidajen.
A nasa jawabin, shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa Alhaji Aminu Zakari ya ja hankalin shugabannin kananan hukumomin jihar da su dauki nauyin cikakkiyar kulawa ga gidajen bisa la’akari da dinbin kudaden da aka kashe wajen gyara gidajen.
Usman Mohammed Zaria