Aminiya:
2025-11-02@17:09:43 GMT

An haramta wa makarantu tilasta wa iyaye sayen sabbin litattafai duk shekara

Published: 6th, September 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Filato, ta haramta wa makarantu a jihar tilasta iyayen ɗalibai sayen sabbin littattafai duk shekara.

Wannan mataki ya biyo bayan ƙudurin da Hon. Joseph Bukar, ɗan majalisa mai wakiltar Shendam ya gabatar, tare da goyon bayan Hon. Mathew Kwarpo Sylvanus daga Mangu ta Kudu.

Sarkin Zazzau ya jagoranci jama’a domin murnar Maulidin bana Gwamnatin Sakkwato ta bai wa ’yan gudun hijira tallafin kuɗi da shinkafa

Bukar, ya ce bai dace ba a ci gaba da tilasta wa iyaye siyan sabbin littattafai duk shekara, inda ya ce hakan cin zarafi ne.

’Yan majalisar sun ce wannan mataki zai rage wa iyaye nauyin kashe kudi.

Sun bayyana cewa ana iya sake amfani da littattafai, har ma a raba wa ’yan uwa da abokan arziƙi.

Majalisar ta amince da cewa:

1. Iyaye su samu ’yancin sayen littattafai daga ko ina, ba dole sai a makarantu ba.

2. An riƙa amfani da littattafai aƙalla shekaru huɗu, kamar yadda ake yi a jihohin Edo da Imo.

3. Makarantu da ƙungiyoyin iyayen ɗalibai su kafa bankin littattafai da tsarin musayar littattafai domin rage kashe kuɗi.

Majalisar ta kuma yi Allah-wadai da al’adar yin bikin kammala makaranta a matakin firamare da ajin ’yan yara.

Ta bayyana cewa hakan ɓata lokaci da kuɗi ne, kuma ba shi da amfani ga ilimi.

Domin tabbatar da bin dokar, majalisar ta umarci kwamitin ilimi da ya kira shugabannin makarantu masu zaman kansu tare da jami’an ma’aikatar ilimi, don sanar da wannan matsaya.

An kuma gargaɗi makarantu cewa duk wanda ya saɓa wa wannan umarni za a hukunta shi.

Hakazalika, majalisar ta tattauna kan matsalar dillalan gidaje waɗanda ba su lasisi.

’Yan majalisar sun koka da yadda ake cutar da jama’a ta hanyar tatsarsu maƙudan kuɗaɗe.

Don haka, an amince da haramta ayyukan dillalai waɗanda ba su da lasisi tare da samar da sabon tsari domin maye gurbin tsohuwar dokar haya.

Kakakin majalisar, Rt. Hon. Naanlong Daniel, ya yaba wa ’yan majalisar bisa gudunmawarsu, tare da tabbatar da cewa majalisar za ta ci gaba da samar da dokoki da za su kawo sauƙi da ci gaban al’ummar Filato.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai iyaye Majalisar Dokoki makarantu majalisar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Shugaba Bola Tinubu ya yi wa sabbin Shugabannin Sojoji ado da karin girma domin su dace da sabbin muƙamansu. Sabbin shugabannin rundunar sojin kasar da aka yi wa ado sun hada da Laftanar Janar, wanda yanzu ya zama Janar Olufemi Olatubosun Oluyede, a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS); da kuma Manjo Janar yanzu ya koma Laftanar Janar Emmanuel Undiendeye Undiendeye a matsayin Babban Hafsan Tsaro na farin kaya (CDI). Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  Sauran su ne Manjo Janar, wanda yanzu ya zama Laftanar Janar Waidi Shaibu a matsayin Babban Hafsan Soja (COAS); Air Vice Marshal, wanda yanzu ya zama Air Marshal Kevin Aneke a matsayin Babban Hafsan Sojan Sama; da kuma Rear Admiral, wanda yanzu ya zama Vice Admiral Idi Abbas a matsayin Babban Hafsan Sojan Ruwa. Shugaba Tinubu ya sanar da maye gurbin Shugabannin Rundunar tsaron ne a ranar Juma’ar da ta gabata, wani mataki da aka danganta da bukatar sake mai da hankali da kuma karfafa tsaron kasa. Bayan haka, Shugaba Tinubu ya bukaci sabbin Shugabannin Rundunar tsaron da su dauki mataki mai tsauri kan barazanar tsaro da ke tasowa a fadin kasar, yana mai gargadin cewa ‘yan Nijeriya na tsammanin ganin sakamako, ba uzuri ba. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai