An haramta wa makarantu tilasta wa iyaye sayen sabbin litattafai duk shekara
Published: 6th, September 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Filato, ta haramta wa makarantu a jihar tilasta iyayen ɗalibai sayen sabbin littattafai duk shekara.
Wannan mataki ya biyo bayan ƙudurin da Hon. Joseph Bukar, ɗan majalisa mai wakiltar Shendam ya gabatar, tare da goyon bayan Hon. Mathew Kwarpo Sylvanus daga Mangu ta Kudu.
Sarkin Zazzau ya jagoranci jama’a domin murnar Maulidin bana Gwamnatin Sakkwato ta bai wa ’yan gudun hijira tallafin kuɗi da shinkafaBukar, ya ce bai dace ba a ci gaba da tilasta wa iyaye siyan sabbin littattafai duk shekara, inda ya ce hakan cin zarafi ne.
’Yan majalisar sun ce wannan mataki zai rage wa iyaye nauyin kashe kudi.
Sun bayyana cewa ana iya sake amfani da littattafai, har ma a raba wa ’yan uwa da abokan arziƙi.
Majalisar ta amince da cewa:
1. Iyaye su samu ’yancin sayen littattafai daga ko ina, ba dole sai a makarantu ba.
2. An riƙa amfani da littattafai aƙalla shekaru huɗu, kamar yadda ake yi a jihohin Edo da Imo.
3. Makarantu da ƙungiyoyin iyayen ɗalibai su kafa bankin littattafai da tsarin musayar littattafai domin rage kashe kuɗi.
Majalisar ta kuma yi Allah-wadai da al’adar yin bikin kammala makaranta a matakin firamare da ajin ’yan yara.
Ta bayyana cewa hakan ɓata lokaci da kuɗi ne, kuma ba shi da amfani ga ilimi.
Domin tabbatar da bin dokar, majalisar ta umarci kwamitin ilimi da ya kira shugabannin makarantu masu zaman kansu tare da jami’an ma’aikatar ilimi, don sanar da wannan matsaya.
An kuma gargaɗi makarantu cewa duk wanda ya saɓa wa wannan umarni za a hukunta shi.
Hakazalika, majalisar ta tattauna kan matsalar dillalan gidaje waɗanda ba su lasisi.
’Yan majalisar sun koka da yadda ake cutar da jama’a ta hanyar tatsarsu maƙudan kuɗaɗe.
Don haka, an amince da haramta ayyukan dillalai waɗanda ba su da lasisi tare da samar da sabon tsari domin maye gurbin tsohuwar dokar haya.
Kakakin majalisar, Rt. Hon. Naanlong Daniel, ya yaba wa ’yan majalisar bisa gudunmawarsu, tare da tabbatar da cewa majalisar za ta ci gaba da samar da dokoki da za su kawo sauƙi da ci gaban al’ummar Filato.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai iyaye Majalisar Dokoki makarantu majalisar ta
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
Rahotanni sun bayyana cewa kasar iran ta bayyana sabbin kayayyaki guda 5 da ta kera a wajen babban taron kere-kere na kasa da kasa karo na 23,kuma dukkansu kamfanonin kasar iran ne suka yi su domin rage dogaro da kayyakin kasashen waje.
Taron ya samu halartar mataimakin shugaban hukumar kula da kimiya da fasaha ta kasa da sauran shuwagabannin kamfanoni inda ya nuna irin karfin iran wajen kere-kere da kuma mayar da hankali kan kamfanoni dake filin shakatawa na pardis technology park.
Daga cikin magungunan da aka gabatar a wajen akwai Sirolimus wanda Zist takhmir company ya kera, kuma magungunan rigakafi ne da ake amfani da su wajen hana dashen gabobin jiki da kuma kula da cututtuka da ba kasafai ake samun su ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan September 16, 2025 Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida September 16, 2025 Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya September 16, 2025 An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci