Leadership News Hausa:
2025-11-02@21:51:22 GMT

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Published: 5th, September 2025 GMT

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

A ranar 3 ga watan Satumba, Sin ta gudanar da babban bikin faretin soja a birnin Beijing, don tunawa da cika shekaru 80 da yakin da Sinawa suka yi da mamayar Japan kana yakin duniya na kin tafarkin murdiya. Wannan bikin faretin soja ya nuna sabbin makamai na zamani na Sin, wadanda suka nuna ci gaban fasahohin tsaron kasar.

Bikin da kuma kayayyakin aikin soja na zamani sun sa wasu mutane shakku: Shin Sin za ta kama hanyar nuna fin karfi? Amsar ita ce, a’a. Kamar yadda wani soja da ya halarci bikin ya ce: “Ba karfi muke nuna ba, sai dai niyyarmu ta kare adalci.”

A wannan bikin faretin soja, rukunin sojojin kiyaye zaman lafiya, ya ja hankalin al’umma sosai. Yawancin sojojin da ke cikin wannan rukuni sun taba yin aikin wanzar da zaman lafiya a kasashen duniya, kamar Sudan ta Kudu, Lebanon, Liberia, Mali, da Jamhuriyar dimokuradiyyar Kongo. Bugu da kari, wannan shekara ce ta cika shekaru 35 da sojojin Sin suka fara shiga ayyukan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya, kuma sojojin kiyaye zaman lafiya na kasar Sin za su ci gaba da kare zaman lafiya a duniya bisa kwarewarsu.

Kwarewar yaki ita ce take iya hana yaki. Kasar Sin ta bunkasa sojojinta ba don nuna fin karfi ne, sai dai don hana yaki, kuma ba don nuna barazana ba, amma don kare zaman lafiya. Daga samar da ka’idoji biyar na yin zama tare cikin lumana har zuwa “kafa al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkanin bil Adam,” daga shiga ayyukan wanzar da zaman lafiya na duniya har zuwa sa kaimin kaddamar da kotun sulhu ta duniya, kullum kasar Sin ta kasance mai kiyaye zaman lafiya da kuma mai kiyaye tsarin duniya.(Mai zane da rubutu: MINA)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

 

Ya kuma bayyana cewa kasar Sin wuri ne mai kyau ga harkokin zuba jari ga ‘yan kasuwa na duniya. Ya ce hadin gwiwa da kasar Sin yana nufin hadin gwiwa da damammaki, imani da kasar Sin yana nufin imani da kyakkyawar makoma, zuba jari a kasar Sin yana nufin zuba jari mai riba ta dogon zango.(Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Maganin Nankarwa (3)
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari