’Yan sandan Kaduna sun gayyaci El-Rufa’i kan zargin yunkurin tayar da zaune tsaye
Published: 5th, September 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna ta gayyaci tsohon Gwamnan jihar, Nasir El-Rufa’i da sauran jagororin jam’iyyar ADC kan zargin yunkurin tayar da zaune tsaye.
A cewar takardar wacce Aminiya ta gani, an gayyace su ne domin su yi wa rundunar bayani kan zargin su da hadin baki da tunzura jama’a wajen tayar da tarzoma da kawo wa zaman lafiya tarnaki a jihar.
Takardar, wacce ke dauke da kwanan watan hudu ga watan Satumban 2025 dai na dauke ne da sa hannun Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda mai kula da Sashen Binciken Manyan Laifuffuka (SCID), Uzairu Abdullahi.
Takardar ta ce, “Wannan sashen namu na bincike a kan wadannan tuhume-tuhumen da ya kunshi ’yan jam’iyyarka. Ana bukatar ka zo tare da su zuwa rundunarnu ranar takwas ga watan Satumba domin ku yi bayani kan zarge-zargen da ake yi muku.
“Wadanda ake gayyatar su ne: Mal. Nasir El-Rufa’i, Bashir Sa’idu, Jafaru Sani, Ubaidullah Mohammed (30), Nasiru Maikano, Aminu Abita da kuma Ahmed Rufa’i Hussaini (Mikiya).”
Da wakilinmu ya tuntubi mataimakin shugaban ADC na kasa shiyyar Arewa maso Yamma, Jafaru Sani, wanda shi ma sunansa na cikin wadanda ake gayyatar, ya ce, galibinsu su ma a kafafen sada zumunta na zamani suka ga labarin gayyatar.
“Haka ne, amma galibinmu ma a kafafen sada zumunta muka ga labarin gayyatar,” in ji Jafarun, yayin da ya ki yin wani karin haske a kan hakan.
A makon da ya gabata ne aka yi musayar yawu tsakanin Gwamnatin Kaduna da tsohon Gwamnan kan wasu ’yan daba da suka kai wa taron jam’aiyyar ADC hari a Kaduna, sannan suka jikkata wasu mahalarta taron.
El-Rufa’is dai ya zargi gwamnatin jihar da aike musu da ’yan dabar a matsayinsu na ’yan adawa, amma ita kuma gwamnatin ta musantanta kuma ce El-Rufa’in ne da kansa ya dauki nauyin hargitsa taron don kawar da tunanin mutane.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda
এছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.
A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan NejaYa bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.
Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.
Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.
TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.
Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.
Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.
Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.