Aminiya:
2025-09-17@23:11:51 GMT

Sojoji sun kashe ’yan Boko Haram 13 a Borno

Published: 4th, September 2025 GMT

Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce, sun kashe mayaƙan Boko Haram 13 bayan da suka yi nasarar daƙile wani harin kwantan ɓauna da ‘yan mayaƙan suka shirya da wasu bama-bamai a kan ayarin sojojin da ke kusa da garin Kareto na Jihar Borno, a ranar Laraba.

Harin dai ya faru ne a yayin da sojoji da ke rakiyar manyan motocin da ke ɗauke da kayan jin ƙai a kan hanyar Gubio zuwa Damasak suka yi ta luguden wuta kan ’yan Boko Haram, bayan tarwatsewar wasu bama-bamai guda biyu.

Hisbah ta kama mai safarar mutane da mata 12 Ganawa da Tinubu: Buƙatun Gwamnonin Arewa maso Gabas

“Sojoji sun ɗauki matsaya cikin gaggawa tare da murƙushe ‘yan tada ƙayar baya da ƙarfin wuta, inda suka kashe 13 nan take,” in ji rundunar OPHK a cikin wata sanarwa.

Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da: Bindigogi ƙirar AK-47 guda takwas da akwatunan albarusai guda 10 da alburusai masu yawa da kuma bama-bamai.

Wani soja ya samu rauni kaɗan, yayin da tayoyin motoci masu sulke huɗu suka lalace sannan wasu manyan motoci biyu suka ƙone.

Sojojin sun ce, an ƙara ƙaimi domin hana masu tada ƙayar baya ’yancin kai hari da kuma tabbatar da kayayyakin jin ƙai sun isa Damasak.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Kareto Rundunar Sojojin Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Shiyyar Kano (KEDCO) ya ƙaryata zargin da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) ya yi masa, dangane da mutuwar wasu marasa lafiya sakamakon katse wutar lantarki da aka ce kamfanin ya yi.

Asibitin na AKTH ya bayyana damuwarsa a ranar Lahadi kan abin da ya kira abin takaici yana mai cewa mutanen da suka mutu za su iya tsira da ransu da ba a ɗauke wutar ba.

Amma a martanin da ya bayar, Shugaban Sashen Hulɗa da Jama’a na KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce asibitin na ƙoƙarin ɓata sunan kamfanin ne kawai, domin an dawo da wutar tun kafin asibitin ya fitar da wannan sanarwar.

Sani ya bayyana cewa matsalar ta samo asali ne daga wani yunƙurin da ake yi na raba ginin asibitin da cibiyoyin lafiya daga gidajen ma’aikatan asibitin.

“Cibiyar asibitin da cibiyoyin lafiya suna da alaƙa da layin 33kV na Zariya Road wanda aka fi ba fifiko wajen raba wuta, kuma suna samun kimanin sa’o’i 22 na wutar lantarki a kullum ƙarƙashin tsarin Band A.

“Amma, shugabannin AKTH sun dage cewa sai gidajen ma’aikata sun ci gaba da kasancewa a layin wutar lantarki ɗaya da cibiyoyin lafiya. Wannan ya janyo barazana ga inganci da kwanciyar hankali na wutar da aka ware wa asibitin.

“An yi ƙoƙari sau da dama don raba gidajen ma’aikata daga cibiyoyin lafiya, amma haƙarmu ba ta kai ga cimma ruwa ba saboda ƙin amincewar shugabannin asibitin. Abin takaici, wannan ya haifar da matsala mai tsanani da ta janyo katsewar wutar da muke ƙoƙarin kaucewa,” in ji KEDCO.

Don tabbatar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga asibitin, kamfanin KEDCO ya ce yana ci gaba da aikin raba layukan wutar lantarkin biyu. Ya ce annan mataki ya zama dole don tabbatar da inganci, tsaro da kyautata lantarki ga asibitin.

Kamfanin ya kuma zargi asibitin da rashin biyan kuɗin wutar lantarki da gidajen ma’aikata ke amfani da ita, wanda ke shafar ingancin ayyukan samar da wuta na kamfanin.

KEDCO ya ce a cikin wata wasiƙa da ya aike ranar 12 ga Agusta, 2025, Babban Jami’in Kasuwanci na kamfanin, Muhammad Aminu Ɗantata, ya sanar da Shugaban Asibitin AKTH game da shirin dakatar da samar da wutar lantarki ga gidajen ma’aikata da wuraren da ba su da muhimmanci, sakamakon rashin cikakken biyan kuɗin wutar wata-wata.

Wasiƙar ta bayyana cewa:

“Duk da roƙon da aka yi sau da dama, asibitin ya ƙi biyan cikakken kuɗin wutar da yake sha a duk wata.

Wannan ya haifar da bashin wutar lantarki da ya kai ₦949,880,922.45 a watan Agustan 2025.

“An bukaci asibitin ya biya kuɗin watan Agusta 2025 na ₦108,957,582.29 gaba ɗaya cikin kwanakin aiki 10, don kaucewa yanke wuta a wuraren da abin ya shafa,” in ji wasiƙar.

Kamfanin ya ƙuduri aniyar ci gaba da samar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga AKTH a matsayin babbar cibiyar lafiya.

A ƙarshe, KEDCO ya roƙi shugabannin asibitin da su ba da haɗin kai a aikin raba layukan wutar, wanda ya ce yana da amfani ga marasa lafiya, ma’aikata, da al’umma baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa