Aminiya:
2025-11-02@19:36:17 GMT

Sojoji sun kashe ’yan Boko Haram 13 a Borno

Published: 4th, September 2025 GMT

Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce, sun kashe mayaƙan Boko Haram 13 bayan da suka yi nasarar daƙile wani harin kwantan ɓauna da ‘yan mayaƙan suka shirya da wasu bama-bamai a kan ayarin sojojin da ke kusa da garin Kareto na Jihar Borno, a ranar Laraba.

Harin dai ya faru ne a yayin da sojoji da ke rakiyar manyan motocin da ke ɗauke da kayan jin ƙai a kan hanyar Gubio zuwa Damasak suka yi ta luguden wuta kan ’yan Boko Haram, bayan tarwatsewar wasu bama-bamai guda biyu.

Hisbah ta kama mai safarar mutane da mata 12 Ganawa da Tinubu: Buƙatun Gwamnonin Arewa maso Gabas

“Sojoji sun ɗauki matsaya cikin gaggawa tare da murƙushe ‘yan tada ƙayar baya da ƙarfin wuta, inda suka kashe 13 nan take,” in ji rundunar OPHK a cikin wata sanarwa.

Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da: Bindigogi ƙirar AK-47 guda takwas da akwatunan albarusai guda 10 da alburusai masu yawa da kuma bama-bamai.

Wani soja ya samu rauni kaɗan, yayin da tayoyin motoci masu sulke huɗu suka lalace sannan wasu manyan motoci biyu suka ƙone.

Sojojin sun ce, an ƙara ƙaimi domin hana masu tada ƙayar baya ’yancin kai hari da kuma tabbatar da kayayyakin jin ƙai sun isa Damasak.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Kareto Rundunar Sojojin Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Duk da cewa gwamnati na da dubban kwararrun malamai a makarantunta, har yanzu ana ganin ɗaliban makarantun gwamnati na kasa da na makarantun masu zaman kansu wajen ƙoƙari da kuma sakamakon jarabawa.

 

Wannan matsala ta daɗe tana jawo muhawara tsakanin iyaye, malamai da hukumomin ilimi.

Wasu na ganin matsaloli ne da ba za su rasa nasaba da rashin kulawa da watsi da harkar ilimi da gwamnati ta yi ba.

Ko wadanne dalilai ne suka daliban makarantun masu zaman kansu suka fi kokari idan aka kwatanta da daliban makarantu na gwamnati?

NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyya

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari