Aminiya:
2025-09-17@23:12:44 GMT

Hisbah ta kama mai safarar mutane da mata 12

Published: 4th, September 2025 GMT

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama wani da ake zargi da safarar mutane (wanda aka sakaya sunansa) a wani wurin garejin motoci tare da wasu mata 12 da ake zargi da safarar mutane da ke shirin tafiya Legas.

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin mataimakin Kwamandan Hukumar ta Hisbah, Sheikh Mujahideen Aminuddeen.

Ganawa da Tinubu: Buƙatun Gwamnonin Arewa maso Gabas Matasa sun kashe ’yan bindiga 6 sun sha alwashin kare kansu

Sanarwar ta bayyana cewa, jami’an rundunar sun kama mutumin ne a wani garejin motoci da ke kan titin Zariya.

Hukumar ta bakin mataimakin ta bayyana cewa, jami’an Hisbah ƙarƙashin jagorancin OC Muhammad Bashir na garejin motoci sun kama wakilin safarar wanda aka ce ya fito daga Jihar Borno, ya hau mota zuwa Legas tare da waɗanda ake zargin.

Aminuddeen ya bayyana cewa, bayanan farko sun nuna cewa, mutumin yana safarar matan ne, kowannensu yana da fasfo na ƙasa da ƙasa zuwa ƙasar Saliyo ta hanyar Legas, Jamhuriyar Benin da Ghana, inda ya ƙara da cewa mutumin yana da shirin yin biza ga waɗanda ya yi safarar don tafiya ƙasar Saudiyya don neman aiki.

Aminuddeen ya kuma bayyana cewa, a yayin da ake yi musu tambayoyi, matan sun sanar da jami’an Hisbah cewa kowaccen su ta biya Naira miliyan 1,500,000 a karon farko tare da yarjejeniyar biyan cikon sauran kuɗi idan sun samu aiki a inda za su.

A cewar hukumar, ɗaya daga cikin matan akwai mai shekara 50 sauran biyu kuma akwai mai shekara 23 da mai shekara 20, yayin da ragowar kuma ’yan shekara 15 ne.

Ya bayyana cewa a cikin waɗanda aka yi safarar, uku sun fito daga Katsina, biyu daga Kano, ɗaya daga jihohin Borno, Jigawa da Zamfara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Hisbah Jigawa bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar

Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.

A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.

KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja

Ya bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.

Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.

Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.

TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.

Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”

Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.

Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.

Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar