Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un
Published: 4th, September 2025 GMT
Babban sakataren jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da Kim Jong Un, babban sakataren jam’iyyar ma’aikata ta kasar Koriya ta Arewa, kuma shugaban harkokin gudanarwa na kasar Koriya ta Arewa, a yau Alhamis a birnin Beijing. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare.
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC
Za a gudanar da kwarya-kwaryan taron shugabannin kungiyar APEC karo na 32 a Koriya ta Kudu.
Eduardo Pedrosa, babban daraktan sakatariyar APEC, ya bayyana cewa tun bayan shigarta APEC, Sin ta kasance mamba mai himma da kwazo. Kuma a halin yanzu, tana taka muhimmiyar rawa wajen ba da jagoranci a karkashin tsarin APEC, haka kuma tana mai da hankali kan yadda za a inganta samar da manyan ci gaba a yankin da kuma duniya baki daya.
Eduardo Pedrosa ya bayyana haka ne kwanan nan yayin wata hira da babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG a birnin Gyeongju dake Koriya ta Kudu. Ya kuma yaba da nasarorin da Sin ta samu a tafarkinta na zamanantar da kanta.(Safiyah Ma)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA