Aminiya:
2025-11-02@12:30:14 GMT

An kama wata uwa kan binne jaririyarta a Kebbi

Published: 4th, September 2025 GMT

’Yan sanda a Jihar Kebbi sun kama wata matashiya mai shekara 20, Maryam Atiku, bisa zargin binne jaririyar da ta haifa da ranta a unguwar Nasarawa da ke Kamba a Karamar Hukumar Dandi.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, CSP Nafi’u Abubakar, ya fitar a wannan Larabar.

Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 29 a Neja Dalilin da Najeriya ba ta jin tsoron matakan Trump — Tinubu

Ya ce matashiyar bayan ta haifi jaririyar, ta naɗe ta a cikin wasu zannuwan atamfa guda uku, sannan ta kai ta wani daji da ake kira Malam Yaro a yankin Nasarawa, inda ta tono rami ta binne ta da ranta.

Sai dai a cewar kakakin ’yan sandan, wani manomi mai suna Alhaji Kabiru Muhammad da ya fita aiki a gonarsa da ke kusa da Malam Yaro, ya lura da alamun an tona wani wuri da ya yi kama da ɗan ƙaramin kabari.

Hakan ce ta sanya manomin ya yi kururuwar neman a kawo masa agaji, inda mutane suka taru aka taimaka har aka tono jaririyar da ranta.

Aminiya ta ruwaito cewa an dai garzaya da jaririyar Asibitin Gwamnati na Kamba, inda aka duba lafiyarta aka tabbatar tana cikin ƙoshin lafiya.

Sanarwar ta ce tawagar ’yan sanda daga sashen binciken manyan laifuka na SCID da ke Birnin Kebbi, ta kama matar nan take, kuma ana titsiye ta a yayin bincike ta amsa laifin, wanda babu wata-wata aka gurfanar da ita a kotu.

Kwamishinan ’yan sanda na jihar, CP Bello M. Sani, ya yaba wa matar gwamnan Kebbi, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, bisa alawashin da ta sha na ɗaukar nauyin kula da jaririyar.

Haka kuma, ya gode wa manomin, Alhaji Kabiru Muhammad bisa irin rawar da ya taka wajen ceto jaririyar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jaririya Jihar Kebbi Uwa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai October 30, 2025 Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 
  • Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda