Aminiya:
2025-09-17@23:15:04 GMT

An kama wata uwa kan binne jaririyarta a Kebbi

Published: 4th, September 2025 GMT

’Yan sanda a Jihar Kebbi sun kama wata matashiya mai shekara 20, Maryam Atiku, bisa zargin binne jaririyar da ta haifa da ranta a unguwar Nasarawa da ke Kamba a Karamar Hukumar Dandi.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, CSP Nafi’u Abubakar, ya fitar a wannan Larabar.

Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 29 a Neja Dalilin da Najeriya ba ta jin tsoron matakan Trump — Tinubu

Ya ce matashiyar bayan ta haifi jaririyar, ta naɗe ta a cikin wasu zannuwan atamfa guda uku, sannan ta kai ta wani daji da ake kira Malam Yaro a yankin Nasarawa, inda ta tono rami ta binne ta da ranta.

Sai dai a cewar kakakin ’yan sandan, wani manomi mai suna Alhaji Kabiru Muhammad da ya fita aiki a gonarsa da ke kusa da Malam Yaro, ya lura da alamun an tona wani wuri da ya yi kama da ɗan ƙaramin kabari.

Hakan ce ta sanya manomin ya yi kururuwar neman a kawo masa agaji, inda mutane suka taru aka taimaka har aka tono jaririyar da ranta.

Aminiya ta ruwaito cewa an dai garzaya da jaririyar Asibitin Gwamnati na Kamba, inda aka duba lafiyarta aka tabbatar tana cikin ƙoshin lafiya.

Sanarwar ta ce tawagar ’yan sanda daga sashen binciken manyan laifuka na SCID da ke Birnin Kebbi, ta kama matar nan take, kuma ana titsiye ta a yayin bincike ta amsa laifin, wanda babu wata-wata aka gurfanar da ita a kotu.

Kwamishinan ’yan sanda na jihar, CP Bello M. Sani, ya yaba wa matar gwamnan Kebbi, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, bisa alawashin da ta sha na ɗaukar nauyin kula da jaririyar.

Haka kuma, ya gode wa manomin, Alhaji Kabiru Muhammad bisa irin rawar da ya taka wajen ceto jaririyar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jaririya Jihar Kebbi Uwa

এছাড়াও পড়ুন:

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

A ƙalla fasinjoji 17 ne suka rasa rayukansu bayan wata motar haya ta faɗa cikin wata gada da ta ruguje a kan titin Gwalli da ke ƙaramar hukumar Gummi, jihar Zamfara.

A cewar hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa (FRSC) reshen Zamfara, hatsarin ya faru ne a daren Lahadi lokacin da motar ɗauke da kaya da fasinjoji ta faɗa cikin gadar da ta ruguje. Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, SRC Isah Aliyu, ya tabbatar da lamarin a wata sanarwa da ya fitar.

Kwamandan FRSC na jihar, CC Aliyu Magaji, wanda ya ziyarci wurin hatsarin, ya bayyana matuƙar baƙin cikinsa da asarar rayukan, inda mafi yawansu mata ne. Ya ce hatsarin ya biyo bayan nauyin da aka ɗora wa motar fiye da ƙima da kuma tafiya da daddare.

Hukumar ta gode wa mazauna yankin da suka gaggauta taimakawa wajen ceto wasu daga cikin waɗanda hatsarin ya rutsa da su. Kwamanda Aliyu ya yi ta’aziyya ga gwamnatin Zamfara da al’ummar Gummi, tare da yin kira ga direbobi su rika bin ƙa’idojin hanya da kuma guje wa tuƙa mota da dare domin kare rayuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara