Aminiya:
2025-09-17@22:52:39 GMT

Dalilin da Najeriya ba ta jin tsoron matakan Trump — Tinubu

Published: 3rd, September 2025 GMT

Shugaba Bola Tinubu, ya ce kuɗaɗen da Najeriya ke samu daga hanyoyin da ba na man fetur ba sun isa wajen daƙile tasirin manufofin tattalin arziƙin shugaban Amurka, Donald Trump.

Trump, ya sanya sabbin dokoki, ciki har da haraji masu tsauri, wanda suka jawo suka daga sassa daban-daban na duniya.

Boko Haram ba kiristoci kaɗai suke kashewa a Arewa Maso Gabas — Ndume Kotu ta ɗaure wani mutum kan kashe saurayin ’yarsa a Ekiti

Yayin da yake karɓar tawagar ‘The Buhari Organisation’ ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Nasarawa, Tanko Almakura, a fadar shugaban ƙasa, Tinubu ya ce Najeriya ta riga ta cimma burin samun kuɗaɗenta na shekarar 2024 tun daga watan Agusta.

“Mun riga mun cimma burin samun kuɗin shiga na wannan shekara tun a watan Agusta.

“Kuɗaɗen da ba na man fetur ba ne, ba ma jin tsoron abin da Trump yake yi a can,” in ji shi.

Shugaban ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta daidaita tattalin arzikin ƙasa tare da rage dogaro da man fetur, don haka matsin lamba daga waje ba zai hana ci gaba da samum kuɗaɗen ƙasar ba.

Trump ya sha kiran ƙungiyar OPEC da ta ƙara fitar da adadin mai domin rage farashinsa a duniya.

A watan Yuli, OPEC da abokan haɗin gwiwarta sun amince da ƙara samar da ganga dubu 548 a kowace rana daga watan Agusta.

A watan Afrilu kuma, Trump ya sanya wa ƙasadhe haraji, ciki har da kaso 14 cikin 100 a kan kayayyakin da ake shigo da su daga Najeriya.

Bayan haka ya sanya hannu kan dokar dakatar da rangwamen haraji ga ƙasashe a ƙarƙashin dokar gaggawa ta tattalin arziƙin Amurka.

A shekarar 2023, Najeriya ta fitar da kaya zuwa Amurka da suka kai dala biliyan 6.29.

Daga Cikinsu akwai man fetur mai na dala biliyan 4.73, gas dala miliyan 920, da takin zamani dala miliyan 167.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tattalin Arziƙi

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.

 

Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.

Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.

NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa