Leadership News Hausa:
2025-11-02@16:54:38 GMT

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

Published: 3rd, September 2025 GMT

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a rungumi akidun tabbatar da daidaito da adalci, tare da tsayawa tsayin daka kan tafarkin samar da ci gaba cikin lumana, da kara azamar inganta rayuwar al’umma a ko da yaushe.

Shugaba Xi ya yi kiran ne a yau Laraba, yayin bikin taron tunawa da cika shekaru 80 da cimma nasarar yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan, da yakin duniya na kin tafarkin murdiya.

Xi ya ce, shekaru 80 da suka shude, bayan shafe shekaru 14 ana gwabza kazamin yaki, al’ummar Sinawa sun yi nasarar murkushe dakarun mamaya na kasar Japan, tare da ayyana cimma cikakkiyar nasarar yakin duniya na kin tafarkin murdiya. Wannan muhimmiyar gaba ta tarihi ta sanya al’ummar kasar Sin ficewa daga zurfin tashin hankali tun shiga zamanin wayewar kai zuwa matakin farfadowar kasa, ya kuma kasance muhimmin lokaci na samun ci gaban duniya. Wannan muhimmiyar nasara ta samu ne ta hanyar hadin gwiwar Sinawa da sauran kawaye masu rajin kin tafarkin murdiya da sauran al’ummun kasashen duniya.

Shugaba Xi ya kara da cewa, salon zamanantarwa irin na Sin, na kan tafarkin neman ci gaba bisa lumana. Kuma Sin za ta ci gaba da kasancewa babban karfi na wanzar da zaman lafiya, da daidaito da ci gaban duniya. Kana da sahihiyar zuciya, tana fatan dukkanin sassan kasa da kasa za su koyi darasi daga tarihi, za su mutunta hadin kai, tare da hada hannu wajen ingiza zamanantar da duniya da samar da makoma mai haske ga daukacin bil’adama. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya November 1, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya November 1, 2025 Daga Birnin Sin Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher
  • Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya
  • Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya