Ƙarfafa wasannin gargajiya zai hana matasa aikata laifi — ALGON
Published: 2nd, September 2025 GMT
Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi na Najeriya (ALGON), ta yi kira ga Ƙungiyar ’Yan Jarida Masu Rubuta Labaran Wasanni (SWAN) da ta ƙara mayar da hankali wajen yada labarai kan wasannin gargajiya, irin su langa da kokawa.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe wanda shi ne shugaban ALGON reshen Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, ya bayyana haka ne a lokacin da shugabannin SWAN na jihar suka kai masa ziyarar ban girma, inda suka nemi goyon bayansa kan babban taron bita da ƙungiyar ke shirin gudanarwa.
A cewarsa, ƙara bayar da muhimmanci ga wasannin gargajiya zai taimaka wajen jan hankalin matasa zuwa harkokin ci-gaban rayuwa, tare da rage yawan fadawa cikin laifuka da shan miyagun ƙwayoyi.
Ya kuma shawarci SWAN da ta ƙulla alaƙa da Hukumar Ci-gaban Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC) domin haɗa kai wajen yada labarai kan wasannin da ake gudanarwa a yankunan ƙarƙara.
Muna buƙatar masu fassara a asibitoci — Al’ummar kurame NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Da Mutane Zasu Bi Wajen Neman DiyyaShugaban na ALGON ya tabbatar da cewa ƙungiyarsa za ta ci gaba da tallafa wa SWAN da kuma sauran shirye-shiryen wasanni da suka dace da manufofin gwamnati a jihar.
A nasa jawabin, Sakataren SWAN na jihar, Williams Attah, wanda ya wakilci shugaban ƙungiyar, Mark Nuhu Mabudu, ya gode wa shugaban ALGON bisa alƙawarin goyon baya, tare da tabbatar da cewa ƙungiyar za ta haɗa kai da shi a cikin shirye-shiryenta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Wasanni wasannin gargajiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar
“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.
Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp