Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya
Published: 1st, September 2025 GMT
Kungiyar Liverpool ta cimma yarjejeniya da Newcastle domin ɗaukar ɗan wasan gaba na ƙasar Sweden, Alexander Isak, akan zunzurutun kuɗi fam miliyan 125, wanda zai sanya shi zama ɗan wasa mafi tsada a tarihin gasar Firimiyar Ingila. Rahotanni sun bayyana cewa Isak zai yi gwajin lafiya yau Litinin tare da zakarun Firimiya, kafin a kammala sanarwar a hukumance da misalin ƙarfe 7 na yamma.
A farkon tattaunawar, Newcastle ta dage cewa sai Liverpool ta biya fam miliyan 130 kafin ta sayar da ɗan wasan, amma daga bisani aka amince da fam miliyan 125. Wannan mataki ya biyo bayan kwantiragin shekaru shida da Isak ya amince da shi a baya, inda ya nuna sha’awarsa ta komawa ƙungiyar mai horaswa Arne Slot.
Tun lokacin bazara Liverpool ta fara zawarcin Isak, inda ta fara da tayin fam miliyan 110 da Newcastle ta ƙi amincewa da shi. Bayan tattaunawa mai tsawo, ƙungiyar ta cimma nasarar da take nema, yayin da Newcastle ta yanke shawarar siyar da ɗan wasan don buɗe hanya ga ɗaukar matashin ɗan wasan Jamus, Nick Woltemade.
A cewar rahotanni, Liverpool za ta miƙa riga mai lamba 9 ga Isak, wanda hakan zai ƙara ɗaukaka matsayin sa a ƙungiyar. Idan aka kammala yarjejeniyar, zai kafa tarihi a matsayin ɗan wasan da aka fi kashe kuɗi akansa a gasar Firimiya, alamu kuma sun nuna cewa sanarwa a hukumance daga kungiyar na nan tafe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: fam miliyan
এছাড়াও পড়ুন:
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.
An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.
Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.
An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.
Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.
Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp