Leadership News Hausa:
2025-11-02@18:12:56 GMT

Ko Zuwan Rasha Afirka Zai Inganta Tsaro A Yankin Sahel?

Published: 31st, August 2025 GMT

Ko Zuwan Rasha Afirka Zai Inganta Tsaro A Yankin Sahel?

Hadakar ta wuce batun tattalin arziki kadai, domin a bangaren tsaro ma, Rasha ta yi amfani da lalacewar alaka tsakanin kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar da kasashen yamma, inda ta samu kutsawa cikinsu.

 

Ganin yadda yankin ke fama da matsalolin tsaro, sai Rasha ta aika musu da sojojin haya na Wagner domin taimakon kasashen da makamai da horo.

 

Amma ganin yadda har yanzu kasashen ke ci gaba da fuskantar hare-hare, shin za a iya cewa alaka da Rasha ta yi musu rana?

 

Sababbin kawayen Moscow

Tun a 2021 Rasha ke tura dubban sojoji da makaman da suka kai miliyoyin Dala zuwa Mali da Burkina Faso da Nijar.

Tana haka ne domin taimakon kasashen wajen yaki da matsalolin tsaro da ya dabaibaye yankin Sahel, inda kungiyoyin ‘yanbindiga masu ikirarin jihadi ke amfani da raunin gwamnati da talauci da kiyayyar gwamnatotin kasashen yamma da rikice-rikicen kabilanci a kasashen wajen kutsawa.

Sojojin hayar na Rasha sai suka samu shiga, inda gwamntocin soji a kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar suka rika daga tutar Rasha a tarukansu, wanda hakan ke nuna goyon bayansu da agajin Rasha.

Hakan ya sa kasashen uku suka nisanta kansu daga Faransa, wadda ita ce ta raine su a baya, da ma wasu kasashen na yamma.

Ba kamar sauran kasashen na yamma ba, ita Rasha ta tura musu dakaru da makamai ba tare da wasu sharuda ba, wanda a lokuta da dama ke zuwa da alkawarin tabbatar da mulkin dimokuradiyya.

Dakarun Wagner na Rasha sun isa Mali ne a 2021 bayan sojojin Faransa sun fice daga kasar, inda a shekarar 2023 sojojin Mali tare da taimakon dakarun Wagner suka kwace wani babban sansanin ‘yanwataye da ke arewacin kasar.

Amma tun bayan wannan nasarar, hare-haren kungiyar Jama’at Nusrat al-Islam wal Muslimin (JNIM) mai alaka da al-Kaeda sai suka karu.

A 2024, sama da mutum 70 ne suka rasu, sannan sama da 200 suka ji rauni a harin JNIM a babban birnin Mali, Bamako.

“Zuwan dakarun Wagner bai dakile harkokin kungiyar JNIM ba,” a cewar Hani Nsaibia ta kungiyar ACLED.

A 2023 ne Yebgeny Prigozhin, jagoran Wagner ya rasu a hadarin jirgin sama kwanaki kadan bayan ya yi yunkurin kifar da gwamnatin Bladimir Putin a Rasha.

Sai gwamnatin Rasha ta yi wa dakarun garambawul, sai suka koma dakarun Afirka wato Africa Corps.

A watan Yunin bana ne dakarun na Wagner suka sanar da ficewarsu daga Mali, inda suka ce sun kammala aikin da ya kawo su.

A wani sako da suka fitar a Telegram, sun ce sun “kashe dubban ‘yantawaye da shugabanninsu da suka dade suna addabar fararen hula.”

 

Ci gaba da rikice-rikice

Kamar yadda alkaluman Global Terrorism Inded suka nuna, sun ce yankin Sahel ne “cibiyar ta’addanci” na duniya, kuma a yankin ne aka samu kusan rabin mutuwa da k da alaka da ta’addanci a duniya, wanda ya sa ake tambayar amfanin shigar Rasha cikin lamarin.

Haka kuma gabashin Mali da Burkina Faso sun dade suna fama da matsalar tsaro tun wajajen 2025.

ACLED ta ce an kashe sama da mutum 20,000, sannan sama da miliyan sun rabu da muhallansu.

A Nijar, akwai gomman sojojin Rasha da suke aiki tare da sojojin kasar, amma har yanzu babu wata nasarar a-zo-a-gani.

A watan Maris na bana, an kashe sama da mutum 40 a wani hari da aka kai a masallaci a yammacin Nijar.

Masanin tsaro Adib Saani ya ce mayakan Nijar da Mali da Burkina Faso sun kara kaimi ne saboda ficewar kasashen yamma.

Andre Lebobich, wani mai bincike a cibiyar Clingendael Institute da ke Netherlands, ya ce sojojin Rasha da ke yankin Sahel aiki ya musu yawa, wanda hakan ne ma a cewarsa ya sa JNIM suka fadada zuwa ksashen Togo da Benin.

 

Rashin karfin soji 

Kwararre a fannin tsaro a Yammacin Afirka Hani Nsaibia ya ce sojojin Rasha da ke aiki a yankin Sahel sun yi karanci, wanda hakan ya sa yake ganin ba sa samun nasara.

Rahotanni sun ce an janye wasu sojojin Rasha saboda yakin Ukraine, wanda hakan ya haifar da gibi saboda babu sojojin wanzar da zaman lafiya daga kasashen yamma ba.

“Zai yi wahala sojojin Rasha 2,000 su iya maye gurbin sojojin wanzar da zaman lafiya kimanin 18,000 da ke aiki a yankin a baya,” in ji shi.

A wani taron tsaro a watan jiya, ministan harkokin wajen Rasha, Sergey Labrob ya nanata cewa kasar za ta ci gaba da taimakon kasashen Afirka domin wanzar da zaman lafiya.

Amma masana na ganin magana kawai ba za ta iya wadatar ba, “domin mutanen yankin da dama suna rayuwa ne a kullum a kasa da dala, ga kuma rashin ababen more rayuwa,” in ji masanin tsaron Ghana, Adib Saani.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasashen yamma sojojin Rasha yankin Sahel wanda hakan

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?