Leadership News Hausa:
2025-11-02@06:33:19 GMT

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

Published: 30th, August 2025 GMT

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

“A yayin aikin ceto, wanda aka sace din ya sami raunin harbin bindiga a kafarsa ta hagu bayan ‘yan ta’addan sun bude wuta lokacin da suke kokarin tserewa,” in ji sanarwar.

 

An garzaya da wanda aka ceto zuwa asibiti, kuma a halin yanzu yana samun sauki.

 

Kwamishinan ‘Yansanda, Bello M. Sani, ya yaba wa jarumtar jami’an da ‘yan sa-kai bisa saurin daukar mataki, tare da sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da yaki da miyagun laifuka da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin Jihar Kebbi.

 

“Wannan aikin ceto ya nuna jajircewarmu wajen kawar da miyagun laifuka a jihar. Ba za mu gajiya ba wajen tabbatar da tsaron kowace al’umma,” in ji Sani.

 

Ya kuma yi kira ga jama’a da su kasance masu fadakarwa tare da bayar da hadin kai ga jami’an tsaro ta hanyar samar da sahihan bayanai cikin lokaci, domin hana aikata laifuka.

 

Kwamishinan ya jaddada cewa tsaro nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa, yana mai bayyana cewa hadin kai mai karfi tsakanin jami’an tsaro da jama’a shi ne ginshiki wajen kawo karshen ta’addanci da sauran laifukan da ke barazana ga zaman lafiya a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Ce Ta Fara Biyan Kudaden Kujerun Aikin Hajjin 2026- NAHCON

Hukumar Aikin Hajji ta Kasa NAHCON ta yi kira ga jihohin kasar nan da su yi koyi da Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa wajen tare kujerun aikin hajji domin baiwa Maniyatan su damar sauke farali.

Kwamishina a hukumar mai kula da shiyyar arewa maso yamma , Sheikh Muhammad Bin Usman yayi wannan kiran a lokacin da ya kai ziyarar aiki a Dutse, babban birnin Jihar.

Sheikh Muhammad Bin Usman yayi bayanin cewar, ya zama wajibi ga sauran hukumomin Alhazan kasar nan da su yi koyi da Gwamna Umar Namadi wajen bai wa hukumomin Alhazai bashin kudade domin tare kujerun aikin Hajji ga maniyata.

Yana mai nuni da cewar, a halin yanzu, jihar Jigawa ce ta farko wajen biyan kujerun aikin Hajjin 2026 a fadin kasar nan.

Babban malamin ya kuma yabawa Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa namijin kokarin sa wajen shirye shiryen aikin Hajji akan lokaci.

Da ya waiwayi batun hadaya kuma, Sheikh Bin Usman yace a duk fadin kasar nan, jihar Jigawa ce take da lasisin yin Hadaya ga maniyata.

Ya ce ita kadai ce tilo take samarwa da maniyatan ta masauki a kusa da harami sabanin wasu hukumomin alhazai da suke yayatawa.

A na shi jawabin, Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce wannan shi ne karo na uku da Gwamna Umar Namadi ke bai wa hukumar rancen kudi domin tare kujerun aikin hajji.

Ya ce makasudin bada rancen kudaden shi ne domin bai wa maniyatan jihar damar sauke farali.

A don haka, Labbo yace tuni hukumar ta ci gaba da rijistar maniyatan aikin Hajjin 2026 tare da bada tabbacin hukumar na ci gaba da rike kambunta wajen gabatar da aikin hajjin.

Kazalika, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya shawarci sauran hukumomin Alhazai su kara himma wajen biyan kudaden kujerun da aka ware musu akan lokaci.

Ya kuma yaba wa NAHCON da Gwamnatin jihar bisa hadin kai da goyon bayan da suke baiwa hukumar a kowanne lokaci.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
  • Jihar Jigawa Ce Ta Fara Biyan Kudaden Kujerun Aikin Hajjin 2026- NAHCON
  • Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba