Aminiya:
2025-09-17@23:17:42 GMT

Ƙara Kuɗin Fasfo: Gwamnati na jefa ’yan Najeriya cikin matsi — Obi

Published: 29th, August 2025 GMT

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya soki Gwamnatin Tarayya kan ƙara kuɗin fasfo.

Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), ta ƙara kuɗin fasfo mai shafi 32 zuwa Naira 100,000, yayin da mai shafi 64 ya koma Naira 200,000.

Ambaliya ta raba ƙauyukan Sakkwato 6 da sauran sassan jihar An fara gyaran layin dogon Abuja-Kaduna bayan hatsarin jirgin ƙasa

Obi, ya wallafa wani rubutu a shafinsa na X, inda ya ce wannan ƙarin ba adalci ba ne duba da halin matsin tattalin arziƙi da ake fuskanta.

“Wannan gwamnati kullum na ƙara jefa mutane cikin wahala a maimakon ta sauƙaƙa musu rayuwa,” in ji shi.

“An ƙara kuɗin fasfo sau uku cikin shekaru biyu kacal. Wataƙila Najeriya ce kaɗai ƙasar da fasfo ya fi mafi ƙarancin albashin ma’aikata yawa.”

Obi, ya ce a yanzu sai ma’aikacin gwamnati ya haɗa albashin wata biyu kafin ya samu fasfo.

Wannan sabon ƙari ya zo ƙasa da shekara guda bayan ƙarin da gwamnatin ta yi a watan Agustan 2024, lokacin da fasfo mai shafi 32 ya tashi daga Naira 35,000 zuwa Naira 50,000, yayin da mai shafi 64 ya tashi daga Naira 70,000 zuwa Naira 100,000.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Ƙara Kuɗin Fasfo wahala

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

An garzaya da ita asibiti, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarta.

’Yansanda sun kama Bosede kuma suna bincike a kan lamarin.

Kakakin rundunar, DSP Olusola Ayanlade, ya ce za su tabbatar da adalci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa