Ƙara Kuɗin Fasfo: Gwamnati na jefa ’yan Najeriya cikin matsi — Obi
Published: 29th, August 2025 GMT
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya soki Gwamnatin Tarayya kan ƙara kuɗin fasfo.
Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), ta ƙara kuɗin fasfo mai shafi 32 zuwa Naira 100,000, yayin da mai shafi 64 ya koma Naira 200,000.
Ambaliya ta raba ƙauyukan Sakkwato 6 da sauran sassan jihar An fara gyaran layin dogon Abuja-Kaduna bayan hatsarin jirgin ƙasaObi, ya wallafa wani rubutu a shafinsa na X, inda ya ce wannan ƙarin ba adalci ba ne duba da halin matsin tattalin arziƙi da ake fuskanta.
“Wannan gwamnati kullum na ƙara jefa mutane cikin wahala a maimakon ta sauƙaƙa musu rayuwa,” in ji shi.
“An ƙara kuɗin fasfo sau uku cikin shekaru biyu kacal. Wataƙila Najeriya ce kaɗai ƙasar da fasfo ya fi mafi ƙarancin albashin ma’aikata yawa.”
Obi, ya ce a yanzu sai ma’aikacin gwamnati ya haɗa albashin wata biyu kafin ya samu fasfo.
Wannan sabon ƙari ya zo ƙasa da shekara guda bayan ƙarin da gwamnatin ta yi a watan Agustan 2024, lokacin da fasfo mai shafi 32 ya tashi daga Naira 35,000 zuwa Naira 50,000, yayin da mai shafi 64 ya tashi daga Naira 70,000 zuwa Naira 100,000.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Ƙara Kuɗin Fasfo wahala
এছাড়াও পড়ুন:
Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
An garzaya da ita asibiti, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarta.
’Yansanda sun kama Bosede kuma suna bincike a kan lamarin.
Kakakin rundunar, DSP Olusola Ayanlade, ya ce za su tabbatar da adalci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp