Yadda Aka Gudanar Da Bikin Ranar Hausa Ta Duniya A Kano
Published: 29th, August 2025 GMT
Yana mai cewa: “Da yawa yanzu an manta zaurance ko ba a yi, saboda yanayin yadda zamani yake. Amma a da, musamman ma idan ka je wajen da ka ga sun iya Hausa kuma su ba Hausawa ba ne, za ka iya juya harshe ta amfani da zaurance wajen canza yaren ba tare da wanda ka ke tare da shi ya fahimci me kake faa ba.
Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a (CAS), Dakta Sunusi Yakubu Ahmed, ya bayyana jin dadinsa matuka bisa zabar kwalejin don gudanar da wannan taron.
Dakta Sunusi ya ce: “Tun lokacin da na ga an yi irin wannan taron a Jami’ar Northwest, na bukaci nima ina da burin ace an kawo irin wannan taron wannan kwalejin. Kuma masu shirya wannan taron sun aminta tare da kawo wannan taron nan.”
Dakta Sunusi ya kara da cewa, Hausa harshe ne wanda ya bunkasa matukar gaske ta hanyar da ya yi nisan da ba za a iya cewa ga inda harshen ya tsaya ba.
Ya ci gaba da cewa ire-iren wadannan tarukan ne ke kara fito da muhimmancin harshen a idon duniya, da kuma ga wadanda suke ganin kamar harshen ba shi da amfani.
Ita kuwa Farfesa Maryam Mansur Yola jaddada muhimmancin wannan rana ta yi ga duk wani mai amfani da harshen Hausa.
Farfesa ta ce kamar yadda aka fara bikin jiya ta hanyar bayar da horo ga wadanda suke amfani da harshen musamman a ayyukansu, kamar ‘yan jarida da masu fassara da malaman makaranta, yau kuma za a gudanar da wassanni da kuma nuna wasu daga cikin al’adun Bahaushe.
Farfesa Maryam ta bayyana dalilin da ya sa aka zabi wannan rana don mayar da ita Ranar Hausa ta Duniya, sakamakon ranar ce da aka kirkiri haruffa masu lankwasa da suka hada da ‘d, ‘b, ‘k, da sauransu, wadanda ke matukar dada wa harshen armashi.
Daga cikin wadanda suka gabatar da jawabi a wajen taron, akwai Hon. Sulaiman Mukhtar Ishak, dan Majalisar Jiha mai wakiltar Karamar Hukumar Madobi, wanda kuma shi ne Shugaban Kwamitin Kula da Ilimi na Majalisar Dokoki ta Jihar Kano. Ya jaddada tare da nuna muhimmancin wannan harshe.
Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai Alhaji Sama’ila Ammani Mai Zare da Alhaji Garba Gasash, da Shugabannin Sashen Koyar da Harshen Hausa na manyan makarantun gaba da sikandire na Jihar Kano, da dalibai da malamai daga ciki da wajen jihar.
Masu wake-wake da makada sun nishadantar da mahalarta taron tare da baje basirar da Allah ya ba su ta hanyar amfani da harshen don isar da sako ko kuma bunkasa harshen.
Daga karshen taron an gudanar da wasannin dambe da langa da kuma nuna wasu daga cikin sana’o’in da Malam Bahaushe ke alfahari da su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: wannan taron
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3
Gwamnatin kasar Iran ta sanar da ranar 30 ga watan nuwambar kowacce shekara a matsayin ranar kasa ta tsibirin Abu Musa tumbu babba da tumbu karami da ta karbo daga hannu birtaniya a shekaru da suka gabata, wanda yayi daidai da 9 ga watan Azar na kalandar iraniyawa .
Tsibiran guda 3 da ake takaddama akansu Abu musa da tunbu babba da karami suna yankin tekun fasha ne tsakanin mailand na iran da kuma hadaddiyar daular larabawa, tsibbiran wani bangare ne na kasar iran tun karnoni da suka gabata da ke cike da abubuwa da suka safi doka da tarihi a iran da kuma kasa da kasa.
Iran ta jaddada cewa dukkan wadannan tsibirai guda 3 wani bangare na kasarta da babu tantama akai,don haka ta yi kira ga kasashen larabawa da su guji daukar duk wani mataki akai da zai iya cutar da dangantakar dake tsakaninsu.
A ranar 30 ga watan nuwambar shekara ta 1971 ne dakarun birtaniya suka janye daga tsibiran kuma kwana biyu kafin kafa hadaddiyar daular larabawa a hukumance aka dawo da ikon mallakar tsibiran ga kasar iran bisa doka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci