Leadership News Hausa:
2025-09-17@23:11:55 GMT

Yadda Aka Gudanar Da Bikin Ranar Hausa Ta Duniya A Kano

Published: 29th, August 2025 GMT

Yadda Aka Gudanar Da Bikin Ranar Hausa Ta Duniya A Kano

Yana mai cewa: “Da yawa yanzu an manta zaurance ko ba a yi, saboda yanayin yadda zamani yake. Amma a da, musamman ma idan ka je wajen da ka ga sun iya Hausa kuma su ba Hausawa ba ne, za ka iya juya harshe ta amfani da zaurance wajen canza yaren ba tare da wanda ka ke tare da shi ya fahimci me kake faa ba.

 

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a (CAS), Dakta Sunusi Yakubu Ahmed, ya bayyana jin dadinsa matuka bisa zabar kwalejin don gudanar da wannan taron.

 

Dakta Sunusi ya ce: “Tun lokacin da na ga an yi irin wannan taron a Jami’ar Northwest, na bukaci nima ina da burin ace an kawo irin wannan taron wannan kwalejin. Kuma masu shirya wannan taron sun aminta tare da kawo wannan taron nan.”

 

Dakta Sunusi ya kara da cewa, Hausa harshe ne wanda ya bunkasa matukar gaske ta hanyar da ya yi nisan da ba za a iya cewa ga inda harshen ya tsaya ba.

 

Ya ci gaba da cewa ire-iren wadannan tarukan ne ke kara fito da muhimmancin harshen a idon duniya, da kuma ga wadanda suke ganin kamar harshen ba shi da amfani.

 

Ita kuwa Farfesa Maryam Mansur Yola jaddada muhimmancin wannan rana ta yi ga duk wani mai amfani da harshen Hausa.

 

Farfesa ta ce kamar yadda aka fara bikin jiya ta hanyar bayar da horo ga wadanda suke amfani da harshen musamman a ayyukansu, kamar ‘yan jarida da masu fassara da malaman makaranta, yau kuma za a gudanar da wassanni da kuma nuna wasu daga cikin al’adun Bahaushe.

 

Farfesa Maryam ta bayyana dalilin da ya sa aka zabi wannan rana don mayar da ita Ranar Hausa ta Duniya, sakamakon ranar ce da aka kirkiri haruffa masu lankwasa da suka hada da ‘d, ‘b, ‘k, da sauransu, wadanda ke matukar dada wa harshen armashi.

 

Daga cikin wadanda suka gabatar da jawabi a wajen taron, akwai Hon. Sulaiman Mukhtar Ishak, dan Majalisar Jiha mai wakiltar Karamar Hukumar Madobi, wanda kuma shi ne Shugaban Kwamitin Kula da Ilimi na Majalisar Dokoki ta Jihar Kano. Ya jaddada tare da nuna muhimmancin wannan harshe.

 

Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai Alhaji Sama’ila Ammani Mai Zare da Alhaji Garba Gasash, da Shugabannin Sashen Koyar da Harshen Hausa na manyan makarantun gaba da sikandire na Jihar Kano, da dalibai da malamai daga ciki da wajen jihar.

 

Masu wake-wake da makada sun nishadantar da mahalarta taron tare da baje basirar da Allah ya ba su ta hanyar amfani da harshen don isar da sako ko kuma bunkasa harshen.

 

Daga karshen taron an gudanar da wasannin dambe da langa da kuma nuna wasu daga cikin sana’o’in da Malam Bahaushe ke alfahari da su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wannan taron

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani.

 

Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’ada, a duk shekara fitowar sabuwar doya kan karya farashin wanda yake kasuwa. Sai dai a bana, wasu daililai na sa farashin doya kara hawa.

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”