An kama Ɗan sanda kan harbe soja a Bauchi
Published: 28th, August 2025 GMT
An kama wani Jami’in ɗan sanda bisa kashe wani soja a garin Futuk da ke Ƙaramar hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi.
Muƙaddashin Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar soji, 33 Artillery Brigade, Atang Hallet Solomon, ya tabbatar wa wakilinmu faruwar lamarin.
’Yan majalisar kasar Mexico sun yi naushe-naushe a zauren majalisa Ana zargin miji da kashe matarsa da duka saboda zuwa gona a makareYa ce, jami’in da ake zargin ya harbe sojan har lahira an kuma tsare shi, inda ya ce a halin yanzu ana gudanar da binciken haɗin gwiwa tsakanin ’yan sanda da sojoji.
Hallet ya ce ana ci gaba da tattaunawa tsakanin hukumomin tsaron biyu domin tabbatar da gudanar da cikakken bincike da kuma hana afkuwar lamarin nan gaba.
Mafarauta da ’yan banga a garin Futuk sun ce lamarin ya biyo bayan cece-ku-ce tsakanin jami’an tsaro kan wata motar ɗaukar kaya da ake zargin na wani kamfanin haƙar ma’adinai na ƙasar China ne.
Sun ce, motar da ke ɗauke da ma’adanai daga wurin haƙar ma’adinai na Yalo, an kama ta ne da yammacin ranar Litinin jim kaɗan bayan sallar Magariba.
Shaidu sun ce sojojin na 33 Artillery Brigade da ke Bauchi sun umarci direban motar mai lamba Gombe 676 BLG da ya tsaya a wani shingen bincike da ke Futuk. Da direban ya ƙi amincewa, sai sojojin suka bi su suka tare motar a kusa da wata gada.
Wani da ya buƙaci a sakaya sunansa kuma shaida ne ya ce, a yayin musayar yawu tsakanin sojan da aka harbe da wani jami’in ’yan sandan kwantar da tarzoma (MOPOL) mai muƙamin Insfekta ya harbe wani soja har lahira a garin Futuk da ke Ƙaramar Hukumar Alkaleri ta Jihar Bauchi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.
Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.
Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.
A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.
“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA